Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa JMI ta gina shirinta na makamashin nukliya ne kan fahinta da kuma kundin tsarin mulkin kasar wanda yayi tir da mamaya da kuma babakere.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a safiyar yau Asabar a hubbaren Imam Ruhullah Al-khomaini (q) wanda ya kafa JMI.

Ministan da sauran manya-manyan ma’aikata a ma’aikatar harkokin wajen kasar sun je hubbaren Imam ne don jadda bai’a ko alkawali da shi kan tafiya a kan tafarkin da ya barsu a kai.

A cikin wani wuri a Jawabinsa Ministan ya kara da cewa a cikin kundin tsarin mulkin JMI ya zo kan cewa Iran ba zata danne wata kasa ba kuma ba zata amince da danniyaba, hakama ba zata zalunci wata kasa ba kuma ba zata yarda a zalunceta ba.

Ya ce abinda gwamnatin kasar Amurka take son tayiwa JMI shi ne danniya da zalunci, Kalmar kada ku ce makamacin Uranium kanta danniya ce. Su sun amincewa kansu su mallaki makaman nukliya amma ba zasu amincewa wata kasa ta ma tashe makamashin uranium wanda yarjeniyar NPT ta amince masu su tace ba. Don haka wannan baa bin amincewa ne ga JMI ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

Hukumar lura da sufurin jiragen kasa ta kasar Sin, ta yi hasashen samun adadin zirga-zirgar fasinjoji ta jiragen kasa sama miliyan 80.5, yayin kwanaki biyar na hutun bikin Duanwu ko bikin tseren kwale kwale na bana.

An fara samun dandazon matafiya ta jiragen kasa a kasar Sin tun daga yau Juma’a, kwana guda gabanin kwanakin hutun uku, yayin da ake sa ran kaiwa kololuwar yawan matafiyan a gobe Asabar, inda ake hasashen adadin zirga-zirgar zai kai kusan miliyan 18.3.

Alkaluma daga kamfanin 12306, mai samar da hidimar yankar tikitin jiragen kasa na kasar Sin, sun nuna wuraren da matafiya suka fi yankar tikitin zuwa, wadanda suka hada da biranen Beijing, da Shanghai, da Guangzhou, da Chengdu, da Hangzhou. Sauran su ne Wuhan, da Xi’an, da Nanjing, da Changsha da kuma Zhengzhou. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo
  • Iran Ta Kaddamarda Sabbin Magunguna Har 23 Tare Riga Kafin HPV A Karon Farko A Kasar
  • Masu Zanga Zanga A Libya Sun Bukaci Firai Ministan Kasar Ya Sauka
  • Limamin Sallar Juma’ar Tehran Ya Jaddada Cewa: Babu Wanda Zai Dakatar Da Iran Tace Sinadarin  Uranium
  • Sojojin Yemen Zasu Bullo Da Shirin Takurawa Jiragen Saman Haramtacciyar Kasar Isra’ila  
  • Nukiliya : Iran ta kirayi mai kula da harkokin Ostiriya da ke birnin Tehran kan wasu kalamai na tsokana
  • Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Iran Na Rashin Tunanin Kera Makamin Nukiliya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Hanyar Warware Takaddamar Shirin Makamashin Nukiliyar Iran