Aminiya:
2025-08-13@13:01:46 GMT

An shiga ruɗani yayin da Sanusi II da Bayero ke shirin hawan salla a Kano

Published: 23rd, March 2025 GMT

Al’ummar Jihar Kano, sun shiga shida ruɗani yayin da rikicin Masarautar jihar, ya ɗauki wani sabon salo game da shirin gudanar da bikin hawan salla.

Tsagin sarakunan jihar na 15 da na 16, wato Muhammadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero, sun shirya gudanar da hawan salla duk da shari’ar da ke gudana kan rikicin masarautar.

Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi Mata sun ƙwace kasuwancin kayan lambu a Gombe

Lamarin ya ɗauki sabon salo ne, bayan wata wasiƙa daga Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya fitar kan shirinsa na yin hawan salla a bana.

Wasiƙar, wacce sakataren Sarkin, Abdullahi Haruna Kwaru, ya sanya wa hannu, an aike wa Kwamishinan ’Yan Sandan Kano, inda ya bayyana shirinsa na gudanar da hawan salla.

Daga cikin hawan da ya bayyana cewar zai yi akwai Hawan Daushe, da Hawan Nassarawa a ranakun 2 da 3 ga watan Shawwal 1446 bayan hijira.

Wannan na zuwa ne bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya umarci Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, da ya fara shirin gudanar da hawan salla.

A cikin wasiƙarsa, Aminu Ado, ya ce wannan hawan na da muhimmanci a gare shi saboda zai cika shekarj biyar da zama sarki.

An jima ba a gudanar da bikin hawan salla ba a Kano saboda fargabar abin da ka iya faruwa tsakanin mabiyan sarakunan biyu.

Rikicin ya fara ne bayan da tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ya tuɓe Sanusi II daga sarauta, tare da naɗa Aminu Ado a matsayin Sarkin Kano.

Sai dai a shekarar 2024, Majalisar Dokokin Kano, ta sake sauya dokar masarautar tare da rushe dukkannin masarautu biyar da Ganduje ya ƙirƙira, tare da mayar da Sanusi II a matsayin Sarki.

Wannan ya janyo ce-ce-ku-ce da tashin hankali a jihar, lamarin da ya sanya tsagin Aminu Ado tafiya kotu.

Kotu ta yanke hukuncin cewa komai ya ci gaba da zama a yadda yake har zuwa lokacin da Kotun Ƙoli za ta yanke hukuncin ƙarshe, lamarin da ya sa dukkanin ɓangarorin biyu ke iƙirarin suna da iko a kan sarautar.

Har yanzu, gwamnatin Kano da Sanusi II ba su ce komai ba kan wasiƙar da Aminu Ado, ya aike wa ’yan sanda, kuma har yanzu ba a ji ta bakin rundunar ’yan sandan jihar ba.

Sai dai, jama’a na nuna damuwa kan abin da ka iya faruwa.

Malam Haladu Bello, wani dattijo mai shekaru 78 a duniya, ya bayyana damuwarsa kan cewa lamarin zai iya haifar da rikici.

“Na sha ganin hawan salla mai ƙyatarwa da kuma wanda ke da matsaloli, amma wannan yana da ban tsoro.

“Abin takaici ne yadda shugabanninmu ke watsi da hatsarin da jama’a ke fuskanta.”

Wani matashi mai shekaru 30, Alhaji Usman Shehu, ya bayyana cewa wannan rikicin cikin gida ne, ba wai abu ne da zai sa mutane cikin fargaba ba.

Ya ce: “Kullum cikin fargabar abin da zai biyo baya muke. Wannan ba daidai ba ne. A bar mu, mu more al’adunmu cikin zaman lafiya.”

Yayin da bikin salla ke ƙara ƙaratowa, al’ummar Kano na ci gaba da fargabar abin da ka iya faruwa idan duka sarakunan biyu suka ci gaba da shirinsu na gudanar da hawan salla.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Aminu Ado Bayero Fargaba gwamna hawan salla Rikicin Masarauta Ruɗani gudanar da hawan salla a gudanar da

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Gudanar Da Zaman Taro Kan Aniyar ‘Yan Sahayoniyya Kan Gaza

Kasashen Turai biyar na kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya sun ki amincewa da matakin mamaye Gaza

Wakilin dindindin na Slovenia ya gabatar da wata sanarwa ga kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya a madadin Burtaniya, Faransa, Denmark, da Girka, yana mai cewa: “A matsayinsu na kasashen Birtaniya, Denmark, Faransa, Girka, da Slovenia, sun kira taron gaggawa na kwamitin tsaron Majalisar kan halin da ake ciki a Gaza. Suna Allah wadai da matakin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta dauka na fadada ayyukanta na soji a Gaza. Ya kuma jaddada cewa: Hakan yana barazana tare da keta dokokin kasa da kasa, yana mai kiran gwamnatin mamayar Isra’ila da ta hanzarta janyewa daga wannan matsayi.

 Ya jaddada cewa: Duk wani matakin mamaye yankunan Falasdinawa da gwamnatin mamayar Isra’ila zata yi yana matsayin keta dokokin kasa da kasa kuma fadada ayyukan soji a yankin zai wurga rayukan fararen hula cikin hatsari, ciki har da rayukan fursunonin yahudawan sahayoniyya da suke hannu ‘yan gwagwarmaya.

Har ila yau, kungiyar agaji ta Red Cross ta yi gargadin cewa: Ana fama da yunwa a Gaza, kuma yara na mutuwa saboda yunwa. Yunwa ta kai wani matsayi mai tsananin gaske wanda fararen hula masu matsananciyar wahala ke jefa rayuwarsu cikin kasada a wuraren raba kayan agaji domin ciyar da iyalansu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza August 11, 2025 Israila Ta Kashe ‘Yan Jarida 4 A Harin Da Ta Kai Kan Tantinsu A Gaza August 11, 2025 Iran: Ba a yanke wani abu game da tattaunawa da Washington ba August 11, 2025 Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza August 11, 2025 Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari August 11, 2025 Chadi: An Daure Wani Dan Adawa Shekaru 20 A Gidan Kaso Da tara August 10, 2025 Dangantaka Tsakanin Iran da Saudiya Yana Taimakawa Zaman Lafiya A yankin August 10, 2025 Iran Zata Hana Amurka Samar da Hanya A yankin Caucasus Ko Rasha Bata taimaka ba August 10, 2025 HKI Ta Kai Hare-Hare A Kan Garuruwa Da Dama A Yankin Quneitra Na Kasar Siriya August 10, 2025 An Zabi Alkalan Wasa Biyu Daga Kasar Iran Don Alkalanci A gasar Kwallon Kafa ta Mata August 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
  • Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 
  • Bankin Duniya zai kashe $300m domin inganta rayuwar ’yan gudun hijira a Arewacin Nijeriya
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Mata Da Matasa
  • Za a gyara tarbiyar tubabbun ’yan daban Kano
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Gudanar Da Zaman Taro Kan Aniyar ‘Yan Sahayoniyya Kan Gaza
  • U Reporters Sun Gudanar Da Taron Wayar Da Kan Jama’a Game Da Shayarwa A Kano
  • Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan
  • Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza