APC ta buƙaci a soke zaɓen cike gurbi a Kano
Published: 16th, August 2025 GMT
Jam’iyyar APC ta buƙaci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), da ta soke zaɓen cike gurbi na Shanono/Bagwai da kuma na mazaɓar Ghari a Jihar Kano.
Jam’iyyar ta buƙaci a soke zaɓen saboda ta zargi cewar an samu tashe-tashen hankula a yankunan da zaɓen ya gudana.
An kama ’yan daba 288 yayin zaɓen cike gurbi a Kano Zaɓen cike gurbi: An kama ’yan daba 100 a Bagwai — INECA cikin wata sanarwa da kakakin jam’iyyar na ƙasa, Felix Morka ya sanya wa hannu, jam’iyyar ta ce ta samu rahotannin da suka tabbatar an samu rikici a Shanono, Bagwai da Ghari.
Ta ƙara da cewa masu kaɗa ƙuri’a sun tsere daga rumfunan zaɓe sakamakon tashin hankali, yayin da jami’an tsaro suka kasa shawo kan lamarin.
“APC na kira ga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da ta gaggauta soke zaɓukan cike gurbi na Shanono/Bagwai da kuma zaɓen mazaɓar Ghari a Jihar Kano saboda tashin hankali da kuma tada hargitsin ’yan daba da aka samu.
“’Yan daba ɗauke da makamai sun tarwatsa rumfunan zaɓe da dama,” in ji sanarwar.
Jam’iyyar ta ƙara da cewa barin zaɓukan su ci gaba da gudana ya saɓa wa tsarin gudanar da zaɓe cikin ’yanci da adalci, kuma hakan zai iya zama barazana ga zaɓuka a gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bagwai Ghari Zaɓen Cike Gurbi zaɓen cike gurbi soke zaɓen
এছাড়াও পড়ুন:
Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC
Hukumar Zabe ta Kasa INEC ta sanar da kammala duk shirye-shiryen zaben ciki gurbi a kananan hukumomin Bagwai, Shanono da kuma Ghari (Kunchi) da ke Kano wanda za a gudanar a ranar Asabar.
Kwamishinan INEC a Kano, Zango Abdu, wanda ya tabbatar da hakan a yayin taron manema labarai, ya ce an riga an raba kayan zabe masu muhimmanci da wadanda ba su da muhimmanci a kananan hukumomi da abin ya shafa.
Tinubu ya cancanci yabo kan daidaita tattalin arzikin Nijeriya —Ngozi An kama Mai Unguwa kan yi wa yarinya fyaɗe a GombeYa ce, “Tun kusan makonni uku da suka gabata aka riga da tura kayayyakin da ba su da muhimmanci wadanda aka tanadar wa mazabu da rumfunan zabe.
“Yanzu haka kayan zaben masu muhimmanci sun iso, kuma za a tura su kananan hukumomi yau da yamma tare da wakilan jam’iyyun siyasa da jami’an tsaro.”
Ya kuma bayyana cewa an kammala horas da dukkan ma’aikatan wucin gadi kuma an tura su wuraren da za su yi aikin, yayin da jami’an tsaro karkashin kwamitin tsaro na haɗin gwiwa sun ba da tabbacin duk wasu tanade-tanade da suka kamata.
Da yake karin haske, Zango ya ce duk na’urorin BVAS wadanda za a yi amfani da su wajen tantance masu kada kuri’a su ma an tanade su tare da tabbatar da nagartarsu.
Ya jaddada kudirin INEC na gudanar da sahihin zabe na gaskiya da adalci, inda ya ce hukumar za ta sanar da wanda ya yi nasara ne kawai bisa kuri’un da aka kada.
“Babbar damuwarmu a yanzu ita ce ’yan siyasa. Amma dai su ma sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, sun kuma shaida mana za su yi zabe cikin lumana. Saboda kwanciyar hankali ne kawai zai ba ’yan kasa ’yancin zaben shugabanninsu,” in ji shi.
Dangane da yadda za a tattara sakamako, Zango ya ce za a bayyana sakamakon akwatuna a duk rumfunan zabe kafin a kai shi cibiyoyin tattarawa na mazabu.
Ana iya tuna cewa, tun a watan Yunin da ya gabata ne INEC ta ayyana 16 ga watan Agustan bana, a matsayin ranar da za a gudanar da zaben cike gurbi a kananan hukumomin na Kano.
Za a gudanar da zaben ne sakamakon rasuwar dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Bagwai da Shonono, Halilu Ibrahim Kundila na jam’iyyar APC, wanda ya riga mu gidan gaskiya a ranar 6 ga watan Afrilun 2024.
Sai dai kuma za a gudanar da zaben cike gurbin ne a Karamar Hukumar Ghari — wadda a baya ake kira Kunc— a rumfunan zabe 10 da masu kada kuria 5200 bisa umarnin kotu.