‘Yan majalisar dokokin Aljeriya sun yi kira da a haramta daidaita alaka da Isra’ila
Published: 23rd, April 2025 GMT
‘Yan majalisar dokokin Aljeriya, sun yi kira da a haramta daidaita alaka da Isra’ila.
‘Yan majalisar dokokin Aljeriya da wakilan jama’a na kasar a zaman majalisar dokokin kasar, sun yi Allah wadai da laifukan da Isra’ila ke aikatawa akan al’ummar Gaza, tare da nuna cikakken goyan bayansu ga falasdinawa.
Mahalarta taron sun yi kira ga majalisar dokokin kasar da ta yi amfani da dokar da ta haramta daidaita alaka da gwamnatin mamayar Isra’ila.
Mustapha Yahi, sakatare-janar na National Democratic Rally (RND) ne ya bayyana haka a wata hira da ya yi da wakilin jaridar Al-Alam: inda yake cewa “Mun sake yin Allah wadai da ci gaba da ta’addancin isra’ila.
Abdelaali Hassani Cherif, shugaban kungiyar Movement of Society for Peace (MSP), ya jaddada bukatar karfafa hadin gwiwa na cikin gida don tinkarar zaluncin da kasashen yammaci da wasu kasashe ke yi a yankin t ahnayar goyon bayan matsayar Aljeriya kan batun Falasdinu.
Kusan shekaru uku da suka gabata, a cikin 2022, ‘yan majalisar dokokin Aljeriya sun kirkiro wani shiri na haramta duk wani yunkuri ko shiri na daidaitawa da Isra’ila.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: majalisar dokokin Aljeriya da Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
Ya kuma tuna irin muhimmiyar rawar da Majalisar tarayya ta taka a lokuta masu sarƙaƙiya a tarihin Nijeriya, ciki har da daƙile shirin ƙara wa’adi na uku da kuma kafa “Dokar Bukata” lokacin rasuwar tsohon shugaban ƙasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp