An kama shi da N25m na sayen kuri’u a zaɓen Kaduna
Published: 16th, August 2025 GMT
Jami’an tsaro sun kama wani mutum da tsabar kuɗi Naira miliyan 25 da ake zargin kuɗin sayen kuri’a ne a zaɓen cike gurbin da ke gudana a Jihar Kaduna.
Da misalin ƙarfe 3 na dare kafin wayewar garin safiyar Asabar da ake gudanar da zaɓen ne ’yan sanda da jami’an hukumar tsaro ta DSS suka kama mutumin a wani otel da ke hanyar Turunku a cikin birnin Kaduna.
A cewar rundunar ’yan sandan binciken farko da aka gudanar ya tabbatar da cewa wanda ake zargin ya shirya yin amfani da kuɗaɗen ne wajen sayen kuri’u
A yayin da ake yi masa tambayoyi, wanda ke ya amsa laifinsa kuma ya roki a yi masa sassauci.
A wata sanarwa da kakaki rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar, Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Rabi’u Muhammad, ya yaba wa haɗin gwiwar jami’an tsaro, inda ya bayyana kama mutumin a matsayin wani muhimmin mataki na kare martabar zabe.
Ya kuma yi gargaɗin cewa duk wanda aka kama yana ƙoƙarin kawo cikas ga zaben, zai fuskanci hukunci ba tare da la’akari da matsayinsa ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: sayen kuri u Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi
A yau Juma’a ne kasar Japan ta gudanar da gangamin tunawa da wadanda suka rasa rayukansu yayin yakin duniya na biyu, sai dai yayin da yake jawabi albarkacin taron, firaministan kasar Shigeru Ishiba, bai tabo batu kan alhakin dake rataye a wuyan kasarsa ba, a matsayinta na wadda ta mamayi wasu kasashen nahiyar Asiya. A hannu guda kuma ya gabatar da addu’a ga wurin ibadar nan na Yasukuni, a matsayin girmmawa ga wurin ibadar da ake kallo a matsayin wurin da aka karrama mutanen da suka tafka danyen aiki yayin yakin duniya na biyu. Kazalika, wasu ministocin kasar sun kaiwa wurin ibadar na Yasukuni ziyarar girmamawa.
Jerin wadannan matakai dai na shan suka, da adawa daga sassan kasa da kasa. Inda wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar game da hakan ta nuna cewa, kaso 64.4 bisa dari na masu bayyana ra’ayin na adawa da ziyarar ‘yan siyasar na Japan zuwa wurin ibadar. Kana kaso 55.3 bisa dari sun soki lamirin Japan bisa yadda ta kawar da kai daga abun da ya auku na tarihin wurin. Kazalika, kaso 65.2 bisa dari sun soki matakin Japan na sauya bayanai dake kunshe cikin litattafan tarihi masu nasaba da batun. Sai kuma kaso 65.7 bisa dari da suka yi kira ga gwamnatin Japan da ta nemi afuwar kasashen da mamayarta ta cutar tare da biyansu diyya.
Wannan dai batu ya haifar da bayyana matukar rashin jin dadi tsakanin al’ummun nahiyar Asiya, ciki har da al’ummun Koriya ta Kudu, da sukarsu game da hakan ya haura kaso 90 bisa dari. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp