Fursunoni 16 sun tsere daga gidan yarin Keffi
Published: 13th, August 2025 GMT
Ana fargabar cewa wasu fursunoni 16 sun tsere daga gidan yarin Keffi da ke Jihar Nasarawa bayan wani kwantan bauna da suka yi wa gandirebobi.
Wata sanarwa da mai magana da yawun Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali a Nijeriya, Umar Abubakar, ta ce fursunonin da ke gidan sun yi wa ma’aikatan da ke tsaronsu rubdugu, lamarin da ya bai wa mutane 16 damar guduwa a safiyar wannan Talatar.
Sanarwar ta ce biyu daga cikin jami’ai biyar da suka ji rauni a yayin harin na cikin mawuyacin hali, kuma yanzu haka ana duba lafiyarsu a wani asibitin gwamnati.
Ya kara da cewa an kamo mutumin bakwai daga cikin waɗanda suka tsere yayin da ake ci gaba da neman ragowar fursunoni tara.
Sanarwar ta ambato cewa Kwanturola-Janar na Hukumar Gidajen Gyaran Hali a Nijeriya, NCoS, Sylvester Nwakuche, ya ziyarci wurin bayan faruwar lamarin, inda ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike tare da gargaɗin cewa duk wani ma’aikaci da aka samu da hannu zai kuka da kansa.
Haka kuma, Nwakuche ya ba da umarnin a gaggauta fita samamen haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro domin kamo waɗanda suka tsere.
Mahukunta sun yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu, tare da neman su hanzarta bayar da rahoton duk wani motsi ko alamar mutanen da suka tsere ga ofishin tsaro mafi kusa.
A ‘yan shekarun nan dai, an samu tserewar fursunoni a Nijeriya lokuta daban-daban, inda a bara kaɗai, fursunoni 118 sun tsere daga gidan gyaran hali na Suleja a Jihar Neja, bayan ruwan sama mai karfi ya lalata bangon gidan yarin da ake cewa daɗewarsa ce ta janyo rushewar ginin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gidan Yarin Keffi Jihar Nasarawa
এছাড়াও পড়ুন:
Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
Gwamnan Jihar Kebbi, Nasiru Idris, ya ce ko sisi gwamnati ba ta biya waɗanda suka yi garkuwa da ɗalibai mata 25 na sakandaren gwamnati ta Maga da ke jihar ba.
Ya bayyana hakan ne a taron manema labarai da aka gudanar a fadar gwamnatin jihar a ranar Talata, inda ya tabbatar da kubutar da ɗaliban da aka sace a farkon makon nan.
Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a KebbiYa ce, “An karɓo ɗalibanmu da aka yi garkuwa da su a Maga. Shugaban ƙasa ya ba jami’an tsaro umarni su gano inda yaran suke, kuma su kubutar da su. Muna tabbatar wa iyayen yara da al’ummar Kebbi cewa ’ya’yansu sun dawo lafiya.
“Muna godiya ga shugaban ƙasa da jami’an tsaro, musamman sojoji, ’yan sanda, da Civil Defence da suka yi aiki tukuru har aka kubutar da yaran cikin ƙoshin lafiya,” in ji Gwamnan.
Idris ya jaddada cewa gwamnatin Kebbi ba ta biya kuɗin fansa ba, “Mu, a matsayin gwamnati, ba mu ba da ko sisi ba. A binciken da muka yi, babu wanda ya biya kuɗin fansar yaran.”
A ranar Litinin din da ta gabata ce ’yqn bindiga suka sace ɗaliban su 25 daga makarantar bayan sun kashe mataimakin shugaban makarantar.
Sai dai daga bisani ɗaya daga cikin ɗaliban ta gudo ’yan kwanaki bayan sace su.