A yayin da yake martani kan suka da ake yi masa na rashin gabatar da kudirori a gaban majalisar, ya bayyana cewa, “tun da na je Majalisar, ba bu wani dan mazabata da ya rubuto min wani kudiri ko bukata da zan gabatar a gaban Majalisa, duk zarge-zargen karya ne suke yi min, kuma idan har akwai, wani ya fito ya kalubalance ni,” inji shi.

 

“Hatta gabatar da kudirori da korafe-korafe a majalisar, wasu sai sun amso cin hancin kimanin naira miliyan 1, ko naira miliyan 2, ko naira miliyan 3, domin karantawa a zauren majalisar, bayan an karanta kudirin, kuma dole sai sun bibiyi ‘yan majalisa sama da 360 domin su goyi bayan a amince da kudirin.”

 

Dan majalisar ya kuma yi watsi da zarge-zargen da ake masa na cewa, ya yi watsi da shirye-shiryen tallafawa matasa a mazabarsa, inda ya ce galibin ayyukan da yake yi suna amfanar da matasa kai tsaye.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu

Yan Majalisar Tarayya daga yankin Kudu sun yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi wa jagoran ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, afuwa bayan da kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.

Kungiyar ’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu maso Gabas ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya yi amfani da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi, wajen yi wa Nnamdi Kanu afuwa wanda kotu ta same shi da laifin ta’addanci.

Alƙali James Omotosho na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ne ya yanke hukuncin, inda ya same shi da laifi a kan tuhumar da ake masa guda bakwai, sannan ya yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

Tuni aka tura Nnamdi Kanu zuwa gidan yari a Jihar Sakkwato inda yake zaman waƙafi.

A cikin sanarwa bayan taron gaggawa da suka gudanar a Abuja, ’yan majalisar sun ce duk da cewa suna girmama kotu da tsarin shari’a, lamarin ya rikiɗe zuwa matsalar ƙasa mai tasiri ga rayuwar jama’a, tattalin arziki da tsaro.

Da yake karanta sanarwar, Hon. Iduma Igariwey ya ce yin afuwa zai taimaka wajen rage tashin hankali da dawo da zaman lafiya a yankin.

Sun lissafa dalilai guda huɗu da suka sa suka yi wannan kira.

Dalilan da suke bayyana su ne ƙaruwa da rashin tsaro da tashin hankali da ke da alaƙa da tsare Kanu; Wahalar rayuwa da tattalin arziki da jama’a ke fuskanta da kuma buƙatar shugabanci mai tausayawa wajen shawo kan matsalolin ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • Gwamna Namadi Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 900 ga Majalisa
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila