Aminiya:
2025-11-27@21:54:54 GMT

Yadda noma ya kankama bayan sulhu da ’yan bindigar Katsina

Published: 16th, August 2025 GMT

A wasu yankunan Jihar Katsina da suka daɗe cikin fargaba da hare-haren ’yan bindiga, zaman lafiya ya fara dawowa sakamakon sulhu da al’umma suka yi da masu tayar da ƙayar baya.

Wannan sulhu, wanda ba a haɗa gwamnati ba, ya bai wa manoma damar komawa gonakinsu cikin daminar bana.

Manoma sun fara noma cikin kwanciyar hankali

Ƙananan hukumomin Batsari, Jibiya da Ɗanmusa na daga cikin wuraren da aka samu wannan ci gaba.

Wasu manoma da wakilinmu ya zanta da su sun bayyana farin cikinsu da yadda rayuwa ke dawowa dai-dai.

Malam Rabe, manomi daga Nasarawa a Ƙaramar Hukumar Jibiya, ya ce: “Mu kam yanzu sai mu ce Alhamdulillahi. Lallai sulhu alheri ne a tsakanin al’umma. Ni rabon da na duƙa gonata da sunan noma na fi shekara 8. Amma yanzu gashi ni ne har da yin ɓaɓar shanu.”

Ya ƙara da cewa:  “Jiya sai kusan magariba na baro gona, wanda can baya ƙarfe sha biyu ba ta yi mani. Rabinmu duk hijira muka yi, tun daga nan har Bugaje, Gangara, Zandam da sauran yankuna.”

Sulhu da ’yan bindiga ya sauya fasalin rayuwa

Alhaji Surajo Jibiya, ɗaya daga cikin masu shirya sulhun, ya ce:  “Mun ga canji sosai. Manomanmu duk sun koma gona. Hatta cikin lunguna mun samu labarin sun ci gaba da noma ba tare da wata fargaba ba. Duk inda ba a yi noma ba shekaru biyar da suka wuce, wannan shekarar an yi fiye da tunani.”

A cewar Surajo, hatta tsohon jagoran ’yan bindiga, Abdu Lanƙai, ya koma noma.

“Duk wata yarjejeniyar da aka yi da shi Lanƙai yana bin ta sau da ƙafa. In ya gano mai laifi, zai yanke hukunci nan take.”

Noman kankana ya kankama a Jibiya

Malam Salisu, mazaunin kan iyakar Jibiya da Batsari, ya ce:  “Har waɗanda ba su yi noman kankana ba a baya, yanzu sun yi kuma an fitar da ita zuwa Abuja da sauran kasuwanni. Duk wata matsala da muke tunanin za ta kunno kai, Allah cikin ikon shi har yanzu babu wata matsala da aka samu.”

Koyi da Batsari aka yi

A Batsari, inda aka fara sulhun, ana tafiya da yarjejeniyar yadda ya kamata. Hassan Dogon Faci ya ce:  “Garuruwan da suka kusan zama kufai kamar Batsarin Alhaji, Watangakiyya, Ɗangeza, Zamfarawa, Madogara, Nahuta, Kofa da Dumburawa — a yanzu duk noma ake yi a cikinsu kuma babu wata matsala.”

Ya ƙara da cewa: “Ranar Juma’ar da ta wuce har wa’azi muka je muka yi a garin Labo. Ashe sai mu ce, an samu nasara. Yanzu sai dai mu ji labari ana fama da matsala, amma mu kam Alhamdulillahi.”

Da sauran rina a kaba

Duk da wannan ci gaba, wasu yankuna kamar Ƙanƙara, Bakori, Faskari, Malumfashi da Ƙafur na ci gaba da fuskantar hare-hare. A kwanan nan, an yi garkuwa da mutane akalla goma sha takwas daga Ƙanƙara zuwa Sheme da Kakumi da sauran yankuna.

Manoman yankunan sun ce duk da akwai gonakin da aka noma, yawancin su na bakin gari ne, amma waɗanda ke nesa sun ɓar gonakin saboda tsoron hare-hare.

 

A cikin ƙananan hukumomin Batsari, Jibiya da ƊanMusa da ke Jihar Katsina, al’umma sun ɗauki matakin da ba a saba gani ba — sun yi sulhu da ’yan bindigar daji, waɗanda suka daɗe suna addabar yankin da garkuwa da mutane, kisan gilla da satar shanu.

Wannan sulhu, wanda ba a haɗa gwamnati ba, ya fara haifar da zaman lafiya da ci gaba.

Manoma sun koma gona

Manoman yankin sun fara komawa gonakinsu cikin daminar bana, suna noma ba tare da fargaba ba. Wasu daga cikinsu sun bayyana cewa sulhun ya kawo sauyi mai ma’ana.

Malam Rabe, wani manomi daga garin Nasarawa a Ƙaramar Hukumar Jibiya, ya ce: “Mu kam yanzu sai mu ce Alhamdulillahi. Lallai sulhu alheri ne a tsakanin al’umma. Ni rabon da na duƙa gonata da sunan noma gaskiya na fi shekara 8, ko in ce 10. Amma yanzu gashi ni ne har da yin huɗar shanu.”

Ya ƙara da cewa:  “Jiya sai kusan magariba na baro gona, wanda can baya ƙarfe sha biyu ba ta yi mani a cikin gonar. Ka san daga bisani rabinmu duk hijira muka yi, tun daga nan har Bugaje, ka tafi har can wajen su Gangara da su Zandam da sauran waɗannan yankuna.”

Sulhu ya canza rayuwa

Alhaji Surajo Jibiya, ɗaya daga cikin masu shirya sulhun, ya ce: “Lallai mun ga canji sosai. Manomanmu duk sun koma gona. Hatta da cikin lunguna mun samu labarin sun ci gaba da noma ba tare da wata fargaba ba. Duk inda ba a yi noma ba shekaru biyar da suka wuce, wannan shekarar an yi fiye da tunani.”

Abin ban mamaki shi ne, tsohon jagoran ’yan bindiga, Abdu Lanƙai, shi ma ya koma noma.

“Duk wata yarjejeniyar da aka yi da shi Lanƙai yana bin ta sau da ƙafa. In ya gano mai laifi, zai yanke hukunci nan take.”

Noman kankana ya kankama a Jibiya

Malam Salisu, mazaunin kan iyakar Jibiya da Batsari, ya ce: “Har waɗanda ba su yi noman kankana ba a baya, yanzu sun yi kuma an fitar da ita zuwa Abuja da sauran kasuwanni. Duk wata matsala da muke tunanin za ta kunno kai, Allah cikin ikon shi har yanzu babu wata matsala da aka samu.”

Batsari ta fara, sauran na bi

A Batsari, inda aka fara sulhun, ana tafiya da yarjejeniyar yadda ya kamata. Hassan Dogon Faci ya ce:

“Garuruwan da suka kusan zama kufai kamar Batsarin Alhaji, Watangakiyya, Ɗangeza, Zamfarawa, Madogara, Nahuta, Kofa da Dumburawa — a yanzu duk noma ake yi a cikinsu kuma babu wata matsala.”

Ya ƙara da cewa: “Ranar Juma’ar da ta wuce har wa’azi muka je muka yi a garin Labo. Ashe sai mu ce, an samu nasara. Yanzu sai dai mu ji labari ana fama da matsala, amma mu kam Alhamdulillahi.”

Da sauran rina a kaba

Ƙaramar Hukumar ƊanMusa ta baya-bayan nan ce da ta yi sulhu, kuma ana ganin tasirinsa. Sai dai a wasu yankuna kamar Ƙanƙara, Bakori, Faskari, Malumfashi da Ƙafur, harin ’yan bindiga bai tsaya ba.

A kwanan nan, an yi garkuwa da mutane akalla goma sha takwas daga Ƙanƙara zuwa Sheme da Kakumi da sauran yankuna.

Manoman yankunan sun ce duk da akwai gonakin da aka noma, yawancin su na bakin gari ne, amma waɗanda ke nesa sun bar gonakin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Batsari Ɗanmusa Jibiya babu wata matsala Ya ƙara da cewa wata matsala da yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta

Kungiyar ta kasa da kasa mai gudanar da a ayyukan agaji, ta sanar da janye ma’aikatanta daga asibitin Darfur, bayan da aka bude musu wuta, ya kuma kai ga kashe daya daga cikin masu aikin agaji.

Kungiyar ta yi kira ga rundunar kai daukin gaggawa RSF da ta tabbatar da tsaro da kuma kiyaye lafiyar ma’aikatan agaji.

Bugu da kari kungiyar ta ce mutumin da aka kashe  a ranar 18 ga watan nan na Nuwamba ma’aikaci ne a ma’aikatar kiwon lafiya ta Sudan.

Asibitin Zalnagi yana a jihar Darfur ta tsakiya ne da a halin yanzu ke karkashin ikon  rundunar “RSF.

A nata gefen, jami’a mai kula da tafiyar da ayyukan kungiyar ta “ Likitoci Ba Tare Da Iyaka Ba.”  Maryam Li Arusi ta ce, babu yadda za a yi ma’aikatansu su ci gaba da gudanar da ayyukansu na jin kai a halin da ake ciki, har sai idan RSF ta bayar da tabbaci da lamunin bayar da kariya ga ma’aikatan da kuma marasa lafiya.

A daya gefen,rundunar RSF ta kore cewa tana cutar da fararen hula, tana mai jaddada cewa duk wanda aka same shi da aikata laifi to za a hukunta shi.

Tun bayan da yankin Darfur ya shiga karkashin ikon rundunar RSF ne ake fito da bayanai akan yadda mayakanta su ka aikata laifukan yaki da cin zarafin mutanen yankin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki November 26, 2025 Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin November 26, 2025 Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah November 26, 2025 UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon November 26, 2025 Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana November 26, 2025 Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu November 26, 2025 Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta November 26, 2025 EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makaamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina