Yadda noma ya kankama bayan sulhu da ’yan bindigar Katsina
Published: 16th, August 2025 GMT
A wasu yankunan Jihar Katsina da suka daɗe cikin fargaba da hare-haren ’yan bindiga, zaman lafiya ya fara dawowa sakamakon sulhu da al’umma suka yi da masu tayar da ƙayar baya.
Wannan sulhu, wanda ba a haɗa gwamnati ba, ya bai wa manoma damar komawa gonakinsu cikin daminar bana.
Manoma sun fara noma cikin kwanciyar hankaliƘananan hukumomin Batsari, Jibiya da Ɗanmusa na daga cikin wuraren da aka samu wannan ci gaba.
Malam Rabe, manomi daga Nasarawa a Ƙaramar Hukumar Jibiya, ya ce: “Mu kam yanzu sai mu ce Alhamdulillahi. Lallai sulhu alheri ne a tsakanin al’umma. Ni rabon da na duƙa gonata da sunan noma na fi shekara 8. Amma yanzu gashi ni ne har da yin ɓaɓar shanu.”
Ya ƙara da cewa: “Jiya sai kusan magariba na baro gona, wanda can baya ƙarfe sha biyu ba ta yi mani. Rabinmu duk hijira muka yi, tun daga nan har Bugaje, Gangara, Zandam da sauran yankuna.”
Sulhu da ’yan bindiga ya sauya fasalin rayuwaAlhaji Surajo Jibiya, ɗaya daga cikin masu shirya sulhun, ya ce: “Mun ga canji sosai. Manomanmu duk sun koma gona. Hatta cikin lunguna mun samu labarin sun ci gaba da noma ba tare da wata fargaba ba. Duk inda ba a yi noma ba shekaru biyar da suka wuce, wannan shekarar an yi fiye da tunani.”
A cewar Surajo, hatta tsohon jagoran ’yan bindiga, Abdu Lanƙai, ya koma noma.
“Duk wata yarjejeniyar da aka yi da shi Lanƙai yana bin ta sau da ƙafa. In ya gano mai laifi, zai yanke hukunci nan take.”
Noman kankana ya kankama a Jibiya
Malam Salisu, mazaunin kan iyakar Jibiya da Batsari, ya ce: “Har waɗanda ba su yi noman kankana ba a baya, yanzu sun yi kuma an fitar da ita zuwa Abuja da sauran kasuwanni. Duk wata matsala da muke tunanin za ta kunno kai, Allah cikin ikon shi har yanzu babu wata matsala da aka samu.”
Koyi da Batsari aka yiA Batsari, inda aka fara sulhun, ana tafiya da yarjejeniyar yadda ya kamata. Hassan Dogon Faci ya ce: “Garuruwan da suka kusan zama kufai kamar Batsarin Alhaji, Watangakiyya, Ɗangeza, Zamfarawa, Madogara, Nahuta, Kofa da Dumburawa — a yanzu duk noma ake yi a cikinsu kuma babu wata matsala.”
Ya ƙara da cewa: “Ranar Juma’ar da ta wuce har wa’azi muka je muka yi a garin Labo. Ashe sai mu ce, an samu nasara. Yanzu sai dai mu ji labari ana fama da matsala, amma mu kam Alhamdulillahi.”
Da sauran rina a kabaDuk da wannan ci gaba, wasu yankuna kamar Ƙanƙara, Bakori, Faskari, Malumfashi da Ƙafur na ci gaba da fuskantar hare-hare. A kwanan nan, an yi garkuwa da mutane akalla goma sha takwas daga Ƙanƙara zuwa Sheme da Kakumi da sauran yankuna.
Manoman yankunan sun ce duk da akwai gonakin da aka noma, yawancin su na bakin gari ne, amma waɗanda ke nesa sun ɓar gonakin saboda tsoron hare-hare.
A cikin ƙananan hukumomin Batsari, Jibiya da ƊanMusa da ke Jihar Katsina, al’umma sun ɗauki matakin da ba a saba gani ba — sun yi sulhu da ’yan bindigar daji, waɗanda suka daɗe suna addabar yankin da garkuwa da mutane, kisan gilla da satar shanu.
Wannan sulhu, wanda ba a haɗa gwamnati ba, ya fara haifar da zaman lafiya da ci gaba.
Manoma sun koma gonaManoman yankin sun fara komawa gonakinsu cikin daminar bana, suna noma ba tare da fargaba ba. Wasu daga cikinsu sun bayyana cewa sulhun ya kawo sauyi mai ma’ana.
Malam Rabe, wani manomi daga garin Nasarawa a Ƙaramar Hukumar Jibiya, ya ce: “Mu kam yanzu sai mu ce Alhamdulillahi. Lallai sulhu alheri ne a tsakanin al’umma. Ni rabon da na duƙa gonata da sunan noma gaskiya na fi shekara 8, ko in ce 10. Amma yanzu gashi ni ne har da yin huɗar shanu.”
Ya ƙara da cewa: “Jiya sai kusan magariba na baro gona, wanda can baya ƙarfe sha biyu ba ta yi mani a cikin gonar. Ka san daga bisani rabinmu duk hijira muka yi, tun daga nan har Bugaje, ka tafi har can wajen su Gangara da su Zandam da sauran waɗannan yankuna.”
Sulhu ya canza rayuwaAlhaji Surajo Jibiya, ɗaya daga cikin masu shirya sulhun, ya ce: “Lallai mun ga canji sosai. Manomanmu duk sun koma gona. Hatta da cikin lunguna mun samu labarin sun ci gaba da noma ba tare da wata fargaba ba. Duk inda ba a yi noma ba shekaru biyar da suka wuce, wannan shekarar an yi fiye da tunani.”
Abin ban mamaki shi ne, tsohon jagoran ’yan bindiga, Abdu Lanƙai, shi ma ya koma noma.
“Duk wata yarjejeniyar da aka yi da shi Lanƙai yana bin ta sau da ƙafa. In ya gano mai laifi, zai yanke hukunci nan take.”
Noman kankana ya kankama a JibiyaMalam Salisu, mazaunin kan iyakar Jibiya da Batsari, ya ce: “Har waɗanda ba su yi noman kankana ba a baya, yanzu sun yi kuma an fitar da ita zuwa Abuja da sauran kasuwanni. Duk wata matsala da muke tunanin za ta kunno kai, Allah cikin ikon shi har yanzu babu wata matsala da aka samu.”
Batsari ta fara, sauran na biA Batsari, inda aka fara sulhun, ana tafiya da yarjejeniyar yadda ya kamata. Hassan Dogon Faci ya ce:
“Garuruwan da suka kusan zama kufai kamar Batsarin Alhaji, Watangakiyya, Ɗangeza, Zamfarawa, Madogara, Nahuta, Kofa da Dumburawa — a yanzu duk noma ake yi a cikinsu kuma babu wata matsala.”
Ya ƙara da cewa: “Ranar Juma’ar da ta wuce har wa’azi muka je muka yi a garin Labo. Ashe sai mu ce, an samu nasara. Yanzu sai dai mu ji labari ana fama da matsala, amma mu kam Alhamdulillahi.”
Da sauran rina a kabaƘaramar Hukumar ƊanMusa ta baya-bayan nan ce da ta yi sulhu, kuma ana ganin tasirinsa. Sai dai a wasu yankuna kamar Ƙanƙara, Bakori, Faskari, Malumfashi da Ƙafur, harin ’yan bindiga bai tsaya ba.
A kwanan nan, an yi garkuwa da mutane akalla goma sha takwas daga Ƙanƙara zuwa Sheme da Kakumi da sauran yankuna.
Manoman yankunan sun ce duk da akwai gonakin da aka noma, yawancin su na bakin gari ne, amma waɗanda ke nesa sun bar gonakin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Batsari Ɗanmusa Jibiya babu wata matsala Ya ƙara da cewa wata matsala da yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
Ta wadanne hanyoyi cutar Kansa ke farawa?
Kowace kwayar halitta ta jikin mutum akwai aikin da take yi, asalin kwayar halittar ta kan kasu kashi-kashi; suna mutuwa idan aka fitar da su ko kuma suka lalace, sai wata kwayar ta maye gurbinsu. A irin wannan lokaci ne, Kansar ke samun gurin zama sai ta zuba tata kwayar halittar ta kori asalin kwayar halittar da ke jikin Dan’adam, wanda hakan ke jawo matsaloli a sassan jikin da Kansar ta kama.
Saboda haka, kwayar cutar Kansa; ta kan watsu a sauran sassan jiki, misali Kansar huhu ta kan tafi cikin kasusuwa ta girma, a yayin da kwayar ta yadu; ana kiranta da suna ‘meh-TAS-tuh-sis’, ita kuma Kansar huhu idan ta tafi cikin kasusuwa; ana kiran ta da suna ‘Lung Cancer’ a turance. A bangaren likitoci, kwayar cutar Kansar da ta shiga cikin kashi; daidai ta ke da ta huhu, sai dai idan ta yadu a cikin kashin.
Banbance-banbancen cutar Kansa:
Wata Kansar ta kan yadu ne cikin gaggawa, yayin da kuma wata ta ke yaduwa a hankali a hankali, sannan kowacce ana iya yin maganinta ta hanyoyi daban-daban, wata ta hanyar tiyata kadai za a iya samun waraka; wata kuma ta hanyar shan magani.
Idan mutum yana dauke da Kansa, likita ya kan yi kokari wajen gano irin Kansar da yake dauke da ita. Mutanen da ke da cutar Kansa, ana yi musu magani ne gwargwadon irin yanayin wadda suke dauke da ita.
Wane matsayi cutar Kansa ta taka?
Duk wanda ke dauke da wannan cuta ta Kansa, likita zai so sanin matakin da ta kai, daga inda ta fara ana kiran sa a turance ‘Cancer Stage’, sannan matsayin da Kansar ta ke shi ne zai taimaka wajen sanin maganin da za a dora mai dauke da lalurar a kai.
Kowace irin Kansa, akwai gwajin da ake yi domin gano matasayin da ta kai. A dokar gwajin matakinta na farko da kuma mataki na biyu, na nuna Kansar ba ta yi karfi sosai ba. Mataki na uku da na hudu kuma yana nuna ta yadu sosai. Mataki na hudu shi ne makura wajen yaduwar ta.
Alamomin 20 Na Kamuwa Da Cutar Kansa:
1- Shashsheka da karancin numfashi
2- Tari da ciwon kirji, alama ce ta Kansar huhu ko ta bargo ciwon kirjin kan kasance daga kirjin zuwa kafada, sannan ya sauko zuwa hannu
3- Zazzabi da saurin kamuwa da ciwo, hakan na faruwa ne dalilin asalin kwayar halittar jinin mutum ta tabu
4- Fama wajen hadiye abu, wannan na nuni da an kamu da wannan cuta
5- Futowar kurji me ruwa a wuya, hammata da kuma gwiwa
6- Yawan zubda jini
7- Kasala da yawan gajiya
8- Kumburin ciki
9- Rashin sha’awar abu da kuma daukewar dandano
10- Ciwon ciki da mara
11- Fitar jini daga dubura
12- Rama lokaci guda
13- Yawan ciwon ciki
14- Nono ya yi ja ya kumbura alama ce ta ‘breast cancer’
15- Canjawar kan nono
16- Nauyi da kuma ciwo na fitar hankali a lokacin al’ada, wannan ita ma alama ce ta ‘uterus cancer’, ana bukatar yin hoto (transbiginal)
17- Kumburin fuska
18- Canjawar farce, zai iya kasancewa ‘lung cancer’, idan kuma ya kode ya yi fari to ‘liber cancer’ ne
19- Ciwon baya a bangaren dama, yana nuni da ‘liber cancer’ ko ‘breast cancer’
20-Fesowar kuraje a jikin mutum
Amma sai an je asibiti an ga likita kafin a tabbatar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA