“Na zo Banga domin jajanta muku bisa wannan mummunan hari. Lokacin da abin ya faru bana nan, sai na umarci mataimakina ya jagoranci tawaga ta musamman domin yi muku ta’aziyya.

“Na dawo Gusau jiya, kuma abu na farko da na fifita yau shi ne zuwa nan da kaina. Gwamnati za ta ƙara ƙoƙari wajen yaƙar ‘yan bindiga,” in ji shi.

Gwamnan ya yi addu’ar Allah Ya ɗauki matakaki a kan waɗanda suka aikata wannan kisan gilla, sannan ya roƙi jama’a da su ci gaba da yin addu’a domin kawo ƙarshen duk wata ɓarna a Zamfara.

Sarkin Kauran Namoda, Dokta Sunusi Ahmad Rashad, wanda ya raka gwamnan, ya yaba masa bisa saurin ɗaukar mataki bayan faruwar lamarin.

“Wannan ziyara tana da matuƙar muhimmanci ga mutanen da abin ya shafa. Muna godiya, kuma Allah Ya ci gaba da maka jagoranci,” in ji shi.

Gwamna Lawal ya kuma yi alƙawarin inganta ayyukan more rayuwa a yankunan, kamar hanyoyi, wutar lantarki, ruwan sha, da sauransu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Hare Hare Yan bindiga Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye

Sakamakon farko na zaben shugaban kasar Jamhuriyar Kamaru da ake ci gaba da kirgawa ya nuna jagoran adawa, Issa Tchiroma Bakary, ya samu gagarumin rinjaye a yankunan da a bayan Shugaba Paul Biya ya saba rinjaye.

Shugaba Paul Biya mai shekaru 92 yana fuskantar abokan hamayya 11 cikin har da tsofaffin mukarrabansa, da ma tsoffin ministocinsa da ke neman kujerarsa da ya shafe shekara 43 a kai kuma yake namen wa’adi na takswas.

Cikinsu har da tsohon Ministan Yawon Bude Ido, Bello Bouba Maigari, da tsohon ministan Ayyuka, Bakary, wanda ya yi murabus a watan Yuli domin shiga takara kuma ya sama mafi shahara bayan doka ta haramta wa madugun adawa Maurice Kamto shiga zaben..

Biya ya ki yin tsokaci game da nasarar a lokacin da ya jefa kuri’arsa a birnin Yaounde ranar Lahadi, amma sakamakon farko sun nuna jam’iyyar FSNC wadda Bakary ya tsaya takara ta samu galaba a yankin da a bayan jam’iyyar CPDM ta Shugaba Biya ke da rinjaye.

Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno

Wani dan jarida da ke aikin sa ido kan zaben shaida wa wakilimu cewa jam’iyyar FSNC ta samu rinjaye a yawancin runfunan zaben da ke larduna bakwai na birnin Yaounde.

Kowacce daga cikin lardunan na da rumfunan zabe 40 zuwa 50, lamarin da ya mayar da Yaounde fage mai matukar muhimmanci a zaben kasar.

Bakary, wanda dan asalin yankin Garoua ne a yankni Arewa mai Nisa ya kuma doke Bello Maigari a yankin da su biyun suka fito.

Amma duk da haka Jam’iyyar CPDM tana bukatar samun gagarumar goyon bayan a yankin Ambazoniya – Arewa mai nisa da kuma yankin Kudu maso Yamma da kuma Arewa maso Yamma masu amfani da turancin Ingilishi.

Wani dan jarida ya bayyana cewa Bakary ya samu rinjaye a kuri’un da aka jefa a kasashen waje, in banda kasar Rasha.

“Karon farko ke nan tun shekarar 1992 da jam’iyyar adawa ta samu irin wannan rinjaye tun da wuri,” in ji shi.

Wadannan alkaluman wucin gadi ne a yayin da ake jihar Hukuamr Shari’a ta kasar za ta sanar da sakamakon zaben a hukumance cikin makonni biyu da ke tafe.

Ya ci gaba da cewa “Hukumar tana iya sauya sakamakon kuma Kotun Koli tana iya nada duk wanda ta ga ya dace da kujerar.”

Tsarin zaben Kamaru na zagaye daya ne, inda duk wanda ya fi samun kuri’u shi ne ke da nasara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara