“Na zo Banga domin jajanta muku bisa wannan mummunan hari. Lokacin da abin ya faru bana nan, sai na umarci mataimakina ya jagoranci tawaga ta musamman domin yi muku ta’aziyya.

“Na dawo Gusau jiya, kuma abu na farko da na fifita yau shi ne zuwa nan da kaina. Gwamnati za ta ƙara ƙoƙari wajen yaƙar ‘yan bindiga,” in ji shi.

Gwamnan ya yi addu’ar Allah Ya ɗauki matakaki a kan waɗanda suka aikata wannan kisan gilla, sannan ya roƙi jama’a da su ci gaba da yin addu’a domin kawo ƙarshen duk wata ɓarna a Zamfara.

Sarkin Kauran Namoda, Dokta Sunusi Ahmad Rashad, wanda ya raka gwamnan, ya yaba masa bisa saurin ɗaukar mataki bayan faruwar lamarin.

“Wannan ziyara tana da matuƙar muhimmanci ga mutanen da abin ya shafa. Muna godiya, kuma Allah Ya ci gaba da maka jagoranci,” in ji shi.

Gwamna Lawal ya kuma yi alƙawarin inganta ayyukan more rayuwa a yankunan, kamar hanyoyi, wutar lantarki, ruwan sha, da sauransu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Hare Hare Yan bindiga Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Jinjinawa NAFDAC Bisa Matsayin Da Ta Taka A Hukumar Lafiya Ta Duniya

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC) murna bisa ci gaba da riƙe matsayin Maturity Level 3 (ML3) na Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) wajen kula da magunguna da rigakafi.

Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Bayani da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, a cikin wata sanarwa, ya bayyana cewa, an gudanar da binciken sake tantance matsayin WHO daga 28 zuwa 30 ga Mayu, 2025, inda aka kimanta NAFDAC bisa ka’idojin ƙasa da ƙasa.

Hukumar ta fara samun wannan matsayi na ML3 ne a 2022, inda ta zama hukumar farko a Afrika mai kula da ƙasashen da ba sa samar da magunguna da ta cimma wannan nasara.

Wannan sabon tantancewa ya biyo bayan wani binciken ne  a watan Nuwamban 2024, tare da gudanar da tarukan duba Shirin Cigaban Cibiyoyi(IDP) guda biyar tsakanin Fabrairu zuwa Afriln 2025 domin tantance matakan gyara. WHO ta yaba wa NAFDAC kan ci gaba da samun tsari mai ƙarfi, da ke aiki yadda ya kamata, tare da yaba wa goyon bayan gwamnati wajen ƙarfafa hukumar.

Shugaba Tinubu ya jinjina wa shugabanni da ma’aikatan NAFDAC bisa ƙwarewa da sadaukarwa, yana mai cewa wannan nasara ta ƙara ɗaukaka matsayin Najeriya a fannin kula da  lafiya da shirin kare cututtuka.

Ya ce wannan nasara na daidai da kudirin gwamnatinsa na Renewed Hope Agenda domin sauya tsarin kula da lafiya.

Shugaban ya yi nuni da ci gaba da ake samu, ciki har da inganta  cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko 17,000, kyautata kulawa da mata masu juna biyu da na’urorin gano cututtuka a yankunan da ba su da iisassun kayayyakin kula da lafiya, horar da ma’aikatan lafiya 120,000, da kuma ninka yawan masu amfani da shirin  inshorar lafiya na ƙasa cikin shekaru uku.

Ya kuma tabbatar da aniyarsa ta ƙarfafa samar da kayayyakin kiwon lafiya a cikin gida da jawo ra’ayin masu zuba jari a fannin lafiya.

Tinubu ya yi alkawarin ci gaba da tallafa wa NAFDAC a yunkurinta na cimma matsayin WHO Maturity Level 4, mafi girma a duniya kan ingancin sarin kula da magunguna.

 

Daga Bello Wakili

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Bukaci Mayar Da Martani Kan Aniyar Isra’ila Ta Mamaye Yankunan Kasashe Domin Kafa ‘Babbar Isra’ila’
  • Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16
  • Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda
  • Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwaman Zamfara
  • Gwamna Namadi Ya Yaba Wa Kungiyar NBA Bisa Inganta Manufofi Da Ka’idojin Aikin Lauya
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto
  • Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.
  • Tinubu Ya Jinjinawa NAFDAC Bisa Matsayin Da Ta Taka A Hukumar Lafiya Ta Duniya