Hakan ya gudana a ƙarƙashin jagorancin hukumomin da ke lura da yadda ake tafiyar da gasar da kuma kare haƙƙin masu amfani da kaya (FCCPC), hukumar kula da tallace-tallace ta Nijeriya (ARCON), da hukumar kula da harkokin caca da wasanni ta Jihar Legas (LSLGA).

Zaɓen ya kasance cikin gaskiya da adalci, inda waɗanda yi nasara suka bar Naira 10,000 a cikin asusun ajiyarsu na Stanbic IBTC ko @ease Wallet har tsawon kwanaki 30.

Daga mata ‘yan kasuwa, zuwa ɗalibai, har zuwa ma’aikatan da suka yi ritaya, waɗanda suka yi nasara yanzu suna iya biyan kuɗin makaranta, fara ƙananan sana’o’i, ko kuma tafiyar da buƙatun gidajensu cikin sauƙi.

An ƙara sanya wasu mutane takwas cikin farin ciki a zaɓen babbar garaɓasar wata huɗu ta farkon shekara wanda aka yi a ranar 7 ga wata.

Mutane bakwai daga kowace shiyya sun samu Naira miliyan ɗaya kowannensu, yayin da babbar kyauta ta wata huɗu ta kai Naira miliyan biyu aka bai wa mutum ɗaya.

Jimillar kyautar ta kai Naira miliyan tara. Hanyoyin da aka bi wajen zaɓar waɗanda suka yi nasara sun nuna irin yadda Bankin Stanbic IBTC ke bai wa kowane mai ajiya muhimmanci.

Zaɓen waɗanda suka yi nasara saboda ajiyar kuɗi a watan Mayun 2025, bankin ya raba Naira miliyan 30 ga mutane 218 a karo na huɗu, yayin da aka raba wa mutane sama da 2,000 Naira miliyan 300 masu asusun ajiya tun fara shirin a shekarar 2021.

Bankin Stanbic IBTC ya kasance ginshiƙi wajen tallafanwa rayuwar ‘yan Nijeriya.

Emmanuel Aihevba, Shugaban Bankin Stanbic IBTC a Nijeriya, ya ce: “Bikin zaɓar waɗanda suka cancanta, ba su kyauta, da yadda aka gudanar da shi a cikin wata biyu, har ma na farkon wata huɗu na bana, ya nuna yadda muke farin ciki da abokan hulɗarmu da suka mayar da hankali kan ajiya. Mun saka wa masu hulɗa da mu 148 zunzurutun kuɗi har Naira miliyan 23 saboda amincewarsu da tafiya tare da mu. Muna son su yi amfani da wannan kuɗi don bunƙasa harkar ilimi ko sana’a.

“A Bankin Stanbic IBTC, muna nuna cewa ya dace mu samar wa abokan hulɗarmu damar bunƙasa rayuwarsu da kuma koya musu yadda za su saba da al’adar ajiyar kuɗi a faɗin Nijeriya.”

Kesena Igben, wani mutum da ya yi ritaya kuma ɗaya daga cikin waɗanda suka yi nasara a gasar, ya bayyana farin cikinsa.

“Na zo tare da ‘yata domin karɓar kyauta. A hanya ta ce, ‘Baba, na ga kana farin ciki.’ Sai na ce mata, ‘Kin san wannan kuɗi zai taimaka min wajen sayen man fetur na mako biyu?’ A gare ni, wannan kyauta ta Bankin Stanbic IBTC babbar alfarma ce, saboda ta rage min damuwar neman kuɗin fetur na mako biyu.”

Yadda Stanbic IBTC ke nuna damuwarsa kan farin cikin abokan hulɗarsa ya nuna yadda suka saka gaskiya da adalci a harkokinsu.

Hukumar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Kaya ta bai wa bankin kyautar ARCON a shekarun 2023 da 2024.

Don haka kai ma shiga cikin jerin waɗanda za su kasance cikin farin ciki!

Ajiye Naira 10,000 kacal ko sama da haka har tsawon kwanaki 30 ko a asusun ajiyarka na Stanbic IBTC ko @ease Wallet domin samun damar shiga sahun waɗanda za su lashe kyautar.

Latsa wannan domin samun damar shiga https://smebanking.stanbicibtc.com/AccountOpening/tier-one ko ka ziyarci kowanne reshen bankin, ka fara daga yau!

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abokan Hulɗa Ajiya Kyauta waɗanda suka yi nasara Naira miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila

Nijeriya da ƙasar Isra’ila sun sake jaddada aniyarsu ta ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro a fannoni masu muhimmanci kamar yaƙi da ta’addanci, musayar bayanan sirri, samar da kuɗin tsaro da kuma horaswa ta musamman.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwar haɗin gwiwa wadda Ƙaramar Ministar Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu, da Mataimakiyar Ministan Harkokin Waje ta Isra’ila, Sharren Haskel-Harpaz suka fitar bayan wani taro na musamman da suka gudanar ranar Litinin a Abuja.

Tinubu na amfani da EFCC ya muzguna wa ’yan adawa — Atiku Amurka da China sun dakatar da harajin da suka ƙaƙaba wa juna

Sanarwar, wadda mai magana da yawun Ofishin Ƙaramar Ministar Harkokin Wajen, Dokta Magnus Eze ya fitar, ta ce taron ya nuna alaƙa mai ɗorewa da muhimmanci tsakanin ƙasashen biyu.

A  yayin taron, wakilan ƙasashen biyu sun tattauna batutuwan da suka shafi tsaro a duniya, musamman yaƙi da ta’addanci, da kuma inganta hulɗar siyasa da tattalin arziki.

Ministocin biyu sun yi ƙara jan hankali kan barazanar ta’addanci a duniya, inda suka ce dole ne ƙasashe su haɗa kai wajen yaƙi da shi, musamman wajen samun bayanai kan hanyoyin samar da kuɗaɗen da ke ɗaukar nauyin ta’addanci.

Mahalarta taron

Haka kuma, ƙasashen biyu sun amince su ƙara haɗin kai a fannonin da suka shafi ƙasa da ƙasa tare da mara wa juna baya a muhimman batutuwa masu kawo ci gaba.

Baya ga tsaro, taron ya mayar da hankali kan amfani da fasaha da ƙirkire-ƙirkire wajen kula da iyakoki, inganta ƙwarewar makamar aiki, musayar al’adu, yawon buɗe ido, noma, da ayyukan jakadanci da shige-da-fice.

Kazalika, ƙasashen sun amince da shirye-shiryen musayar ma’aikata da ziyarar ƙara ilimi, tare da kafa tsari na musamman domin ci gaba da tattaunawa da haɗin gwiwa a nan gaba.

A wani ɓangare na taron, an yi muhawara kan fasahar zamani wadda Ambasada Janet Olisa daga Ma’aikatar Harkokin Waje ta Nijeriya ta jagoranta tare da Ambasada Sharon Bar-Li daga Ma’aikatar Harkokin Waje ta Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila
  • Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Mata Da Matasa
  • ‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno
  • Mahukuntan Iraki Sun Bayyana Cewa: Akwai Yiwuwar Masu Ziyarar Arba’een Na Imam Husaini {a.s} Zasu Zarce Miliyan 4
  • Ya ba wa alaramma kyautar motarsa saboda daɗin karatun Alkur’ani
  • Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • Gwamnatin Kwara Ta Yi Gargadi Ga Manoman Ruwan Malka Na Wata Agusta