Ejodame ya rahoto CAS, yana cewa “Tare da ingantattun jirage da ke da ingantattun tsare-tsaren kai hare-hare na dare, jirgin NAF ya kai hare-hare guda 798”.

 

 

A nasa jawabin, Gwamna Zulum ya yabawa NAF bisa ci gaba da bayar da tallafi ta sama wajen gurgunta karfin ‘yan ta’adda da kuma kare al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila Ta Kashe ‘Yan jaridar Al Jazeera Biyar A Gaza

Rundunar sojin Isra’ila ta ce ta kashe wani fitaccen dan jarida na kafar yada labarai ta Al Jazeera Anas al-Sharif tare da abokan aikinsa hudu a wani hari da ta kai Gaza.

Isra’ila ta zarge shi da kasancewa wani jagora na Hamas sannan ta ce ta hallaka shi saboda irin rahotannin da yake bayarwa masu tsanani daga arewacin Gaza.

Isra’ila ta hari ‘yan jaridar biyar – Anas al-Sharif wanda shi ne fitacce tare da Mohammed Qreiqeh masu aikawa da rahotanni ne sai kuma masu daukar musu hoto Ibrahim Zaher da Mohammed Noufal da kuma Moamen Aliwa wadanda dukkanin su suna aiki ne da kafar ta Al Jazeera.

A lokacin da Isra’ila ta kai musu harin ta sama suna cikin wani tanti ne na ‘yan jarida da ke wajen asibitin al-Shifa a birnin na Gaza.

Isra’ilar ta ce kisan hukunci ne na irin rahotannin da Anas din ya ke aika wa Al Jazeera da ke arewacin Gaza.

Baya haka Isra’ila ta kuma ce dan jaridar wani jigo ne na wani reshe na kungiyar Hamas da ke shirya hare-haren makaman roka da Hamas ke kai mata – zargin da Al Jazeera ta musanta.

A sanarwar da ta fitar rundunar sojin Isra’ilar ta zargi al-Sharif da fakewa a matsayin dan jarida- tana zarginsa da hannu wajen kai mata hare-hare da makaman roka kann fararen hula da sojojinta.

Ta ce a baya ta fitar da wasu bayanan sirri da ke tabbatar da alakarsa da ayyunakn soji na Hamas, ciki har da jerin horon ta’addanci da ya halarta.

Sanarwar ta kara da cewa kafin harin sojin na Isra’ila sun dauki matakai na kauce wa illata farar hulha.

Mako biyu da ya wuce Al Jazeera ta soki rundunar sojojin ta Isra’ila kan abin da ta kira kokarin tunzura masu aika mata da rahotanni a Gaza ciki har da al-Sharif.

Kungiyoyin kare hakkin dan’adam sun ce Isra’ila ta kashe ‚yan jarida sama da dari biyu (200) a Gaza tun daga watan Oktoba na 2023, kan abin da suka ce yunkuri ne na hana bayar da rahotannin zargin cin zarafin da Isra’ila ke yi a Gaza.

Isra’ila dai ta hana ‘yan jarida na waje aikawa da rahotanni a fili daga yankin.

Jim kadan bayan harin ne Isra’ila ta fitar da wata sanarwa da a ciki take tabbatar da kai harin da ta ce ta hallaka Anas al.-Sharif, tana mai cewa wani jagora ne a Hamas.

Rundunar sojin ta Isra’ila ba ta ambaci sauran ‘yan jaridar da ta kashe su tare ba.

Al-Sharif, mai shekara 28, yana rubuta sakonni ne ta shafin X, jim kadan kafin mutuwarsa – inda a ciki yake gargadi kan ruwan bama-bamai da Isra’ila ke yi a birnin na Gaza.

BBC ta ga wasu hotunan bidiyo masu tayar da hankali wadanda kuma ta tabbatar da sahihancinsu, na bayan harin da ya hallaka ‘yan jaridar, inda a ciki ake iya ganin mutane na dauke gawawwakin.

BBC/Hausa

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 
  • Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara
  • Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
  • ‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno
  • Isra’ila Ta Kashe ‘Yan jaridar Al Jazeera Biyar A Gaza
  • An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
  • Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
  • Jami’an Tsaron Iran Sun Murkushe ‘Yan Ta’adda Kan Ofishin ‘Yan Sanda A Kudu Maso Gabashin Kasar