Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9
Published: 14th, August 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta amince a kafa karin sababbin jami’o’i masu zaman kansu guda guda tara a fadin Najeriya.
Ministan Ilimi, Dr Tunji Alausa ne ya sanar da hakan ranar Laraba lokacin da yake jawabi ga ’yan jaridar Fadar Shugaban Kasa jim kadan da kammala taron Majalisar Zartarwa ta Kasa.
Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanciShugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ne ya jagoranci taron wanda aka gudanar a Abuja.
A cewar ministan, sababbin jami’o’in da aka ba lasisin sun hada da Jami’ar Tazkiyah da ke Kaduna, Jami’ar Leadership da ke Abuja, Jami’ar Jimoh Babalola da ke Kwara da Jami’ar Bridget da ke Mbaise a jihar Imo.
Sauran jami’o’in sun hada da jami’ar Greenland da ke Jigawa da jami’ar JEFAP da ke Neja da jami’ar Azione Verde da ke Imo, sai jami’ar karatu daga gida ta Unique da ke jihar Legas da kuma takwararta mai suna American Open University da ke jihar Ogun.
Alausa ya kuma ce Tinubu ya gaji bukatu guda 551 na kafa makarantun gaba da sakandire masu zaman kansu, wadanda ya ce dole sai an cika tsauraran sharuda kafin a ba su lasisin.
Sai dai ya ce rashin cika wadannan sharuda ne ya rage adadin zuwa guda 79 kacal, inda daga ciki aka amince da guda tara a ranar ta Laraba.
Ya ce da yawa daga cikin jami’o’in da aka ba lasisin sun dade suna jira, wasu ma sun shafe sama da shekaru shida suna kan layi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya
এছাড়াও পড়ুন:
El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya sauka sheƙa daga jam’iyyar SDP zuwa jami’yyar haɗaka ta ADC.
Komawar El-Rufai jam’iyyar ADC a hukumance wani mataki ne da ake ganin zai kawo sabon salo a siyasar adawa wajen ƙalubalantar jam’iyyar APC mai mulki a Zaɓen 2027.
An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da OlympiacosA wannan Alhamis ɗin ce El-Rufai ya kammala rajistar zama mamba na jam’iyyar ADC a mazaɓarsa ta Unguwar Sarki da ke birnin Kaduna, inda ya yi alƙawarin amfani da jam’iyyar ADC wajen fuskantar abin da ya kira rashin ƙwarewa a jagorancin gwamnatin jihar.
“Ina da cikakkiyar rajista a jam’iyyar African Democratic Congress,” in ji shi a gaban manyan jami’an jam’iyyar, ciki har da Mataimakin Shugaban ADC na Arewa maso Yamma, Jafaru Sani, da Sakataren Yi wa Mambobi Rajistar Jam’iyyar na Ƙasa, Sanata Sadiq Yar’adua.
A watan Maris na bana ne dai El-Rufai ya sauya sheƙa daga APC zuwa SDP a wani yunƙuri na shirya haɗin gwiwar adawa, sai dai ya ce tattaunawar da suke yi a SDP ɗin ta gaza haifar da ɗa mai ido wajen cimma muradinsu saboda “tsoma bakin gwamnati da kuma cin hanci da wasu shugabannin jam’iyyar ke yi.”
Da yake jawabi kan siyasar Jihar Kaduna, El-Rufai ya yi kira ga jama’a da su yi rajista da ADC domin “maimaita abin da muka yi a 2015,” yana mai zargin gwamnatin APC mai ci da sakaci da jagorancin al’umma.
“Ina kira ga dukkan ’yan Kaduna masu shekaru 18 zuwa sama da su fito su yi rajista. Da ikon Allah, zamu sake kawar da gwamnatin da ta nuna gazawa.
“Mu da muka taimaka muka ɗora su a kujerar mulki, za mu taimaka wajen dawo da su gida… kafin su wuce kotu,” in ji El-Rufai.