An naɗa sabon Sarkin Alkaleri a Bauchi
Published: 13th, August 2025 GMT
Mai martaba Sarkin Bauchi, Alhaji (Dr) Rilwanu Suleiman Adamu, ya naɗa tsohon babban jami’in Hukumar Kwastam mai ritaya, Alhaji Bala Muhammad Gidado, a matsayin Sarkin Alkaleri, wanda zai gaji marigayi Sarkin Alkaleri, Alhaji Muhammad Abdulkadir.
Da yake jawabi yayin naɗin, Sarkin Bauchi ya jaddada cewa sabon Sarkin Alkaleri ya samu wannan muƙami ne bisa la’akari da cancanta, ilimi, gogewa da kuma nagarta.
Ya buƙaci sabon sarkin da ya yi amfani da wannan gogewa wajen ci gaban masarauta, tare da tabbatar da gaskiya, adalci, riƙon amana da haɗin kan jama’a.
Sarkin ya yi addu’ar Allah Ya ƙara zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar Bauchi, tare da yaba wa Gwamna Bala Abdulqadir Muhammad, bisa ayyukan raya ƙasa da inganta tsaro.
A nasa jawabin, shugaban ƙaramar hukumar Alkaleri, Garba Hassan Bajama, ya gode wa Sarkin Bauchi bisa tabbatar da wannan sarauta, yana mai alƙawarta haɗin kai tsakanin gwamnati da masu sarauta wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin.
Bikin naɗin ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ‘yan siyasa, masu riƙe da muƙaman gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki, lamarin da ya nuna muhimmancin mukamin Sarkin Alkaleri a tsarin masarautar Bauchi.
Bayan naɗin, an sanya wa sabon sarki rawani da alkyabba a fadar Sarkin Bauchi, sannan jama’a suka raka shi cikin waƙe-waƙe da kaɗe-kaɗe na farin ciki zuwa garin Alkaleri.
Sabon Sarkin ya isa fadarsa a kan doki, inda aka gudanar da hawan durbar na murnar karɓar sarautar, tare da miƙa masa wuƙa, takobi da Alƙur’ani a matsayin alamar mulki.
Alhaji Bala Muhammad Gidado, wanda ya yi ritaya daga Hukumar Kwastam, yanzu shi ne Sarkin Alkaleri na tara a tarihin masarautar Bauchi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rilwanu Suleiman Adamu Sarkin Alkaleri Sarkin Bauchi Sarkin Alkaleri Sarkin Bauchi sabon Sarkin
এছাড়াও পড়ুন:
Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
Ana zargin wata amarya da yi wa angonta yankan rago kwana uku bayan ɗaurin aurensu a Jihar Katsina.
Angon mai suna Abubakar Abdulkarim da aka fi sani da Dan Gaske, ana zargin ya rasa ransa bayan da amaryar ta yi amfani da wuƙa wajen halaka shi.
Shaidu sun ce ta yi masa mummunan rauni a wuya wanda ya yi sanadiyyar mutuwarsa.
Angon da amaryarsa suka daura aure ne a ranar Alhamis, 18 ga Nuwamba, 2025, amma farin cikin aure ya rikide zuwa makoki a ranar Lahadi da rana lokacin da lamarin ya faru.
Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke FuskantaWani ɗan uwansa mai suna Aminu Danladi ya ce cewa sun yi taro da marigayin da safiyar ranar, suna shirya ziyarar ’yan uwansu da za a kai da yamma.
Ya ce daga baya ango ya koma gida domin shiri, sai kuma aka ji labarin an same shi kwance a cikin jini babu rai.
Aminu ya kuma ƙaryata jita-jitar da ake yaɗawa cewa auren dole ne aka yi wa ma’auratan, inda ya tabbatar da cewa dangantakarsu ta kasance lafiya kafin aure.
Majiyoyi sun ce matar, ’yar asalin Katsina, ta taɓa yin aure a baya, abin da ake zargin dangin mijin ba su sani ba.
An ce bayan faruwar lamarin amaryar ta ruɗe inda ta je gidan maƙwabta tana neman abinci. Wannan hali ya sa tsofaffin mata zargin akwai matsala, suka bi ta gida inda suka tarar da gawar mijin, suka kuma sanar da jami’an tsaro.
Rundunar ’Yan Sanda ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce ta fara gudanar da bincike a kai.
Kakakin ’yan sanda na jihar, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ya ce an kama mutum ɗaya da ake zargi da hannu a lamarin, kuma bincike na ci gaba.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Katsina, CP Bello Shehu, ya tabbatar da cewa za a gudanar da bincike mai zurfi, tare da kira ga jama’a da su bayar da bayanai masu amfani.