Sojoji Sun Kama Mutane 107 Da Ake Zargi, Sun Ceto Mutane 20 A Cikin Maku Guda – DHQ
Published: 14th, August 2025 GMT
A yankin Arewa-maso-Gabas, ya ce sojojin, sun kawar da ‘yan ta’adda da dama, sun lalata sansanonin kayan aikinsu, sun kwato makamai, sun wargaza hanyoyin hada-hadarsu tare da samar da amintaccen wuri don sake tsugunar da ‘yan gudun hijira.
A cewar Kangye, sojojin sun kama mutane 37 da ake zargin ‘yan ta’adda ne, tare da kubutar da mutane biyar da aka yi garkuwa da su, tare da kwato makamai, alburusai, kayayyakin masarufi, motoci da babura, sannan kuma sun warware wasu bama-bamai cikin nasara a yankin.
Da yake ba da rahoto kan yankin Arewa maso Yamma, Kangye ya ce sojoji sun kama mutane 11 da ake zargin ‘yan ta’adda ne tare da kubutar da mutane 17 da aka yi garkuwa da su a wasu hare-hare.
Hakazalika a yankin Arewa ta tsakiya, daraktan ya bayyana cewa sojoji sun kama mutane 15 da ake zargi tare da ceto mutane tara tare da kwato wasu kayayyaki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama matashi kan zargin aikata fashi a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta kama wani matashi mai shekara 18 bisa zargin aikata fashi da makami a jihar.
An kama shi ne a garin Kwadon bayan samun sahihin bayani daga jama’a.
NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa TuraiKakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an kama matashin ne ranar 9 ga watan Agusta, 2025 da misalin ƙarfe 2:30 na rana.
Hakazalika, ya ce an samu ƙunshi ganyen da ake zargin tabar wiwi ne.
Bincike ya nuna cewa matashin na cikin mutanen da ’yan sanda ke nema game da aikata fashi da makami, waɗanda ake shari’arsu a babbar kotun jihar.
A cewar DSP Abdullahi, matashin ya amsa cewa yana daga cikin waɗanda suka kai hare-haren.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Bello Yahaya, ya umsrci a miƙa shi zuwa sashen binciken manyan laifuka domin zurfafa bincike kafin gurfanar da shi a kotu.
Rundunar ta yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba ta bayanai da za su taimaka wajen yaƙar laifuka a jihar.