Jama’a sun koka kan rashin kammala aikin titi a Kafanchan
Published: 13th, August 2025 GMT
Ƙungiyar Ci Gaban Masarautar Jama’a (JEDA), ta roƙi Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, da ya kammala manyan titunan Birnin Kafanchan, wanda aikin ya tsaya tun zamanin Nasir El-Rufai.
Muƙaddashin shugaban ƙungiyar, Ahmad Usman Husain, ya ce waɗannan tituna na da muhimmanci wajen bunƙasa tattalin arziki da rayuwar yau da kullum a Kudancin Kaduna.
Ya ƙara da cewa abin takaici ne a ce ba a haɗa titunan Kafanchan cikin jerin sabbin ayyukan da gwamnan ya ƙaddamar ba, duk da cewa ya yi alƙawarin kammala su a lokacin yaƙin neman zaɓe.
Ƙungiyar ta bayyana Kafanchan a matsayin cibiyar kasuwanci da zamantakewar al’ummar Kudancin Kaduna.
Ta ce titunan na muhimmanci wajen harkokin kasuwanci, lafiya, ilimi da hulɗar jama’a.
JEDA, ta yi kira ga gwamnan da ya cika alƙawuransa, ta hanyar adalci wajen rabon ayyukan ci gaba.
Sannan ya tabbatar da cewa al’ummar Masarautar Jama’a ba a bar su a baya ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jama a Ƙungiya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta bayyana sabbin nasarorin da ta samu wajen yaƙi da laifuka a jihar, ta hanyar holen mutum 34 da ta kama da aikata laifuka daban-daban.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Rabi’u Muhammad, ya ce wannan ci gaba ya samu ne saboda sabbin dabarun aiki da kuma bayanan sirri da aka samu daga al’umma da hukumomin tsaro.
Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000A Anguwar Barnawa da wasu wurare a Kaduna, rundunar Operation Fushin Kada ta kama mutane 13 da ake zargi da aikata fashi da makami da satar wayoyi a otel-otel da gidaje.
An ruwaito sun taɓa kashe ɗan sanda a shekarar 2024, kuma suna samun bayanai daga dilolin miyagun ƙwayoyi a wuraren shaƙatawa. A
An ƙwato bindiga ƙirar gida, gatari da adduna 13, mota, kwamfuta huɗu, wayoyi 13 da talabijin huɗu.
Haka kuma, a Nunbu Bashayi da ke Sanga, an kama mutane bakwai da ake zargi da garkuwa da mutane tare da neman kuɗin fansa.
Dukkanimsu sun amsa laifinsu kuma ana neman ragowar waɗanda suke tsere.
A wani samame daban, ’yan sanda sun kama wasu mutane huɗu da ake zargi da aikata fashi, fyaɗe da damfara.
Sun saba kai hari gidajen mutane, ɗaukar kuɗaɗen mutane, aikata fyaɗe sannan su riƙa ɗaukar bidiyo tsoratar da mutane.
A Zariya kuwa, an kama wasu mutane tara da suka haɗa da maza da mata waɗanda ake zargi da yi wa direban Adaidaita sahu fashi ta hanyar zuba masa magani a abin sha.
Rundunar ta kuma kama wani likitan bogi mai suna Adamu Abubakar Muhammed wanda ya yi wa mutane tiyata ba tare da shaidar karatun likitanci ba.
Ya yi amfani da takardun bogi wajen yin aiki na tsawon wata guda kafin a gano shi.
Kwamishinan, ya ce duk waɗanda aka kama suna hannun rundunar, kuma za a gurfanar da su kotu bayan kammala bincike.
Ya gode wa jami’an tsaro da al’umma kan haɗin kai, inda ya yi da a ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin inganta tsaro a jihar da ƙasa baki ɗaya.