Aminiya:
2025-10-13@15:49:52 GMT

Jama’a sun koka kan rashin kammala aikin titi a Kafanchan

Published: 13th, August 2025 GMT

Ƙungiyar Ci Gaban Masarautar Jama’a (JEDA), ta roƙi Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, da ya kammala manyan titunan Birnin Kafanchan, wanda aikin ya tsaya tun zamanin Nasir El-Rufai.

Muƙaddashin shugaban ƙungiyar, Ahmad Usman Husain, ya ce waɗannan tituna na da muhimmanci wajen bunƙasa tattalin arziki da rayuwar yau da kullum a Kudancin Kaduna.

Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura

Ya ƙara da cewa abin takaici ne a ce ba a haɗa titunan Kafanchan cikin jerin sabbin ayyukan da gwamnan ya ƙaddamar ba, duk da cewa ya yi alƙawarin kammala su a lokacin yaƙin neman zaɓe.

Ƙungiyar ta bayyana Kafanchan a matsayin cibiyar kasuwanci da zamantakewar al’ummar Kudancin Kaduna.

Ta ce titunan na muhimmanci wajen harkokin kasuwanci, lafiya, ilimi da hulɗar jama’a.

JEDA, ta yi kira ga gwamnan da ya cika alƙawuransa, ta hanyar adalci wajen rabon ayyukan ci gaba.

Sannan ya tabbatar da cewa al’ummar Masarautar Jama’a ba a bar su a baya ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jama a Ƙungiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da kyautar motoci ƙirar Hilux guda shida da babura 30 domin taimaka wa sojoji wajen yaƙi da ’yan bindiga a faɗin jihar.

Gwamnan, ya miƙa motocin da baburan ga Kanal Hussaini Rabi’u Toro na rundunar sojoji ta takwas a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.

’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi

Ya ce wannan kyauta na cikin ƙoƙarin gwamnatinsa na tabbatar da tsaro da walwalar al’umma.

“Tsaro shi ne babban abin da gwamnatina ta mayar da hankali a kai. Ba za mu yi wasa da harkar tsaro ba.

“Za mu ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro da dukkanin abin da suke buƙata,” in ji Gwamna Idris.

Ya ƙara da cewa, an fara bai wa sojoji ne kyautar, amma sauran hukumomin tsaro su ma za su samu irin wannan tallafi nan ba da jimawa ba.

Da yake bayani a wajen taron, Kanal Hussaini Toro, ya gode wa gwamnan bisa wannan taimako, inda ya cewa hakan zai ƙara musu ƙaimi wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

“Sojoji sun yi matuƙar farin ciki da wannan tallafi. Zai taimaka wajen inganta aikinmu na tabbatar da tsaro a Jihar Kebbi,” in ji Kanal Toro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato
  • Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina