Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci
Published: 14th, August 2025 GMT
Ƙasar Amurka ta amince ta sayar wa Najeriya makaman da kuɗinsu ya kai Dala miliyan 346, kwatankwacin Naira biliyan 530 don yaƙi da ta’addanci.
Makaman da za a siyar sun haɗa da bama-bamai da na’urorin kakkabo jiragen sama da jirage marasa matuka da sauran su.
NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa TuraiA cewar Kamfanin Sarrafa Makamai na Amurka (DSCA), za a sayar wa Najeriya makaman ne domin tallafa wa shirinta na yaki da ’yan ta’adda da masu safarar miyagun ƙwayoyi.
Kamfanin ya sanar da cinikin ne a cikin wata sanarwa ranar Laraba.
A cewar sanarwar, Najeriya ta buƙaci sayen bama-bamai guda 1,002, na’urar kakkabo jirage guda 1,002, sai manyan bindigu guda guda 5,000 da sauran makamai.
Kazalika, Amurkar ta amince ta sayar wa Najeriya helikwaftocin kai hari guda 12 da sauran muggan makaman da darajarsu ta kai Dala miliyan 997 a 2022.
Kamfanin ya ce kamfanonin da aka amince wa su yi kwangilar dillancin makaman su ne Lockheed Martin da RTX.N da kuma BAE.
“Wannan cinikin zai taimaka wa bunƙasa hulɗar kasa da kasa da kuma manufofin Amurka a kan harkar tsaro da inganta alaƙa da Najeriya a matsayin babbar ƙawa a yanki Afirka yamma da hamadar Sahara,” in ji sanarwar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya a sayar wa Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
A cikin shekarun nan, matsalolin tsaro a Najeriya—kamar ta’addanci, da garkuwa da mutane, da rikicin manoma da makiyaya, da kuma ayyukan ’yan bindiga—suna kara ta’azzara, lamarin da ya sanya al’umma da masana tsaro ke tambayar wace hanya ta fi dacewa gwamatani ta yi amfani da shi wajen kawo karshen wadannan matsaloli da suka ki ci suka ki cinyewa tsawon shekaru.
Yayin da wasu ke ganin amfani da karfin soji ne kadai hanyar da zai kawo karshen wannan matsala, wasu na ganin tattaunawa ne kadai mafita, wasu har ila yau na ganin idan aka yi amfani da gaurayen biyun zai fi dacewa.
NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?Ko wanne daga cikin wadannan hanyoyi ne idan gwamnati ta yi amfai dashi ko da su don magance wannan matsala?
Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan