Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bai wa Gwamnatin Tarayya ranakun 24, 25 da 26 ga watan Satumba domin ta kammala shari’ar da ta shafe shekaru goma tana yi wa tsohon mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Kanal Sambo Dasuki mai ritaya, kan zargin mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma halasta kuɗin haram.

Mai shari’a Peter Lifu ya bayar da wannan umarnin a ranar Talata, bayan amincewa da buƙatar gwamnati ta ɗage zaman domin kawo ƙarin shaidu da kuma ba wa Dasuki damar fara kare kansa.

Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila Tinubu na amfani da EFCC ya muzguna wa ’yan adawa — Atiku

Ya kuma umurci gwamnati ta kira sauran shaidunta domin kammala gabatar da shaida a shari’ar da aka shafe fiye da shekaru goma.

Tun a shekarar 2015 aka kama Dasuki bisa zargin karkatar da dala biliyan 2.1 na kuɗin sayen makamai, inda ya samu ’yanci a ranar jajiberin Kirsimetin shekarar 2019, bayan ce-ce-ku-ce kan ƙin bin umarnin kotuna da dama, ciki har da na Kotun Ƙoli ta ECOWAS, wadda ta ba shi beli.

A zaman da ya gabata, wani mai ba da shaida daga bangaren gwamnati, Monsur Mohammed, wanda shi ne mai kula da kayayyakin shaida a Hukumar Tsaro ta DSS, ya shaida wa kotu cewa jami’an tsaro sun yi bincike a gidajen Dasuki da ke Abuja, Kaduna da Sakkwato bayan cafke shi.

Haka kuma, Dasuki yana fuskantar wata shari’a ta daban a Babbar Kotun Abuja wadda hukumar EFCC ke zarginsa da karkatar da kuɗin makamai na Naira biliyan 19.4.

Sauran wadanda EFCCn ke tuhuma tare da Dasuki sun haɗa da tsohon Ministan Harkokin Kuɗi, Bashir Yuguda, tsohon Gwamnan Sakkwato, Attahiru Bafarawa, da ɗansa Sagir, da kamfaninsu, Dalhatu Investment Limited.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Shari a

এছাড়াও পড়ুন:

Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina

Ana zargin wata amarya da yi wa angonta yankan rago kwana uku bayan ɗaurin aurensu a Jihar Katsina.

Angon mai suna Abubakar Abdulkarim da aka fi sani da Dan Gaske, ana zargin ya rasa ransa bayan da amaryar ta yi amfani da wuƙa wajen halaka shi.

Shaidu sun ce ta yi masa mummunan rauni a wuya wanda ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Angon da amaryarsa suka daura aure ne a ranar Alhamis, 18 ga Nuwamba, 2025, amma farin cikin aure ya rikide zuwa makoki a ranar Lahadi da rana lokacin da lamarin ya faru.

Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta

Wani ɗan uwansa mai suna Aminu Danladi ya ce cewa sun yi taro da marigayin da safiyar ranar, suna shirya ziyarar ’yan uwansu da za a kai da yamma.

Ya ce daga baya ango ya koma gida domin shiri, sai kuma aka ji labarin an same shi kwance a cikin jini babu rai.

Aminu ya kuma ƙaryata jita-jitar da ake yaɗawa cewa auren dole ne aka yi wa ma’auratan, inda ya tabbatar da cewa dangantakarsu ta kasance lafiya kafin aure.

Majiyoyi sun ce matar, ’yar asalin Katsina, ta taɓa yin aure a baya, abin da ake zargin dangin mijin ba su sani ba.

An ce bayan faruwar lamarin amaryar ta ruɗe inda ta je gidan maƙwabta tana neman abinci. Wannan hali ya sa tsofaffin mata zargin akwai matsala, suka bi ta gida inda suka tarar da gawar mijin, suka kuma sanar da jami’an tsaro.

Rundunar ’Yan Sanda ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce ta fara gudanar da bincike a kai.

Kakakin ’yan sanda na jihar, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ya ce an kama mutum ɗaya da ake zargi da hannu a lamarin, kuma bincike na ci gaba.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Katsina, CP Bello Shehu, ya tabbatar da cewa za a gudanar da bincike mai zurfi, tare da kira ga jama’a da su bayar da bayanai masu amfani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya
  • Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu.
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • Faduwar Darajar Kuɗi Na Kara Tsananta Kalubale Ga Kotunan Shari’a — CJN
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • ’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina