Dasuki: Kotu ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin kammala shari’ar kuɗin makamai
Published: 12th, August 2025 GMT
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bai wa Gwamnatin Tarayya ranakun 24, 25 da 26 ga watan Satumba domin ta kammala shari’ar da ta shafe shekaru goma tana yi wa tsohon mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Kanal Sambo Dasuki mai ritaya, kan zargin mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma halasta kuɗin haram.
Mai shari’a Peter Lifu ya bayar da wannan umarnin a ranar Talata, bayan amincewa da buƙatar gwamnati ta ɗage zaman domin kawo ƙarin shaidu da kuma ba wa Dasuki damar fara kare kansa.
Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila Tinubu na amfani da EFCC ya muzguna wa ’yan adawa — AtikuYa kuma umurci gwamnati ta kira sauran shaidunta domin kammala gabatar da shaida a shari’ar da aka shafe fiye da shekaru goma.
Tun a shekarar 2015 aka kama Dasuki bisa zargin karkatar da dala biliyan 2.1 na kuɗin sayen makamai, inda ya samu ’yanci a ranar jajiberin Kirsimetin shekarar 2019, bayan ce-ce-ku-ce kan ƙin bin umarnin kotuna da dama, ciki har da na Kotun Ƙoli ta ECOWAS, wadda ta ba shi beli.
A zaman da ya gabata, wani mai ba da shaida daga bangaren gwamnati, Monsur Mohammed, wanda shi ne mai kula da kayayyakin shaida a Hukumar Tsaro ta DSS, ya shaida wa kotu cewa jami’an tsaro sun yi bincike a gidajen Dasuki da ke Abuja, Kaduna da Sakkwato bayan cafke shi.
Haka kuma, Dasuki yana fuskantar wata shari’a ta daban a Babbar Kotun Abuja wadda hukumar EFCC ke zarginsa da karkatar da kuɗin makamai na Naira biliyan 19.4.
Sauran wadanda EFCCn ke tuhuma tare da Dasuki sun haɗa da tsohon Ministan Harkokin Kuɗi, Bashir Yuguda, tsohon Gwamnan Sakkwato, Attahiru Bafarawa, da ɗansa Sagir, da kamfaninsu, Dalhatu Investment Limited.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Shari a
এছাড়াও পড়ুন:
Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a Isra’ila da Pakistan
Dubban mutane ne suka fito kan tituna a birnin Tel Aviv na Isra’ila ranar Asabar, domin yin kira da a kawo ƙarshen yaƙin Gaza, kwana guda bayan da gwamnatin Isra’ila ta lashi takobin faɗaɗa rikicin tare da ƙwace birnin Gaza.
Masu zanga-zangar da ke riƙe da hotunan waɗanda har yanzu ake garkuwa da su a yankin Falasdinawa sun yi kira ga gwamnati da ta tabbatar da sakin su ’yan uwansu.
Al-Hilal ta ɗauki Nunez daga Liverpool ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki’Yan jaridar AFP a wajen gangamin sun ƙiyasta adadin waɗanda suka halarci taron a matsayin dubbai, yayin da wata ƙungiya da ke wakiltar iyalan wadanda aka yi garkuwa da su ta ce mutane kusan 100,000 ne suka yi dafifi.
Hukumomin ƙasar ba su bada wasu alƙaluma mutane da suka shiga zanga-zangar ba, amma sun hakikance lalai ya, zarta duk wasu gangamin da aka yi a baya na adawa da yakin.
Masu zanga-zangar sun ƙarkare da aike wa Firaminista Benjamin Netanyahu saƙo da kakkausar murya.
Shahar Mor Zahiro, ɗaya daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da ɗan uwansa, ya shaida wa AFP cewar: “Idan ka mamaye sauran sassan Gaza kuma aka kashe sauran ’yan uwanmu da ake garkuwa da su, za mu bi ka har cikin harabar dandalin Square, ko a lokacin yakin neman zaɓe ko a kowane lokaci ko waje.”
A ranar Juma’ar da ta gabata, majalisar ministocin tsaron Netanyahu ta amince da gagarumin farmaki na kwace birnin Gaza, lamarin da ya janyo cece-kuce da tofin Allah tsine daga cikin gida da ƙasashen duniya.
Wasu ƙasashen ketare, ciki har da wasu kawayen Isra’ila, sun yi ta matsa kaimi don ganin an tsagaita wuta domin tabbatar da dawowar wadanda aka yi garkuwa da su da kuma taimakawa wajen rage matsalar jin kai a yankin.
Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasɗinu a IstanbulDubban masu zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu sun taru a Dandalin Beyazit na Istanbul a ranar Asabar bayan sallar Magariba, domin nuna adawarsu ga kisan kiyashi da ƙaƙaba yunwa da Isra’ila ke yi a Gaza.
Gangamin, wanda ya haɗa da ƙungiyoyin ba da gwamnati da kuma jama’a da dama, ya ci gaba da tafiya zuwa Masallaci mai tarihi na Ayasofya.
Mahalarta sun yi ƙoƙarin jan hankalin duniya game da matsalar jin kai da ke faruwa a Gaza, tare da nuna goyon baya gare su, yayin da tashin hankali da ƙarancin abinci da magunguna ke ƙara ta’azzara.
Masu shirya zanga-zangar sun yi kira ga al’ummar duniya da su ɗauki matakan gaggawa don kawo ƙarshen wahalhalun.
Isra’ila Na Fuskantar Matsin Lamba Daga DuniyaIsra’ila na fuskantar ƙarin fushin duniya saboda kisan kiyashi da take yi a Gaza, inda ta kashe fiye da mutane 61,000 tun watan Oktoba 2023.
Haren-haren da soja ke kaiwa sun lalata yankin sosai kuma sun haifar da mutuwa ta hanyar yunwa da ƙunci.
A watan Nuwamba da ya gabata, Kotun Hukunta Laifukan Yaƙi ta Duniya ta bayar da sammacin kama Firayiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da tsohon Ministan Tsaronsa Yoav Gallant saboda laifukan yaƙi da laifukan cin zarafin ɗan adam a Gaza.
Haka kuma, Isra’ila tana fuskantar shari’ar kisan kiyashi a Kotun Duniya saboda yaƙin da take yi a yankin.