Aminiya:
2025-10-13@17:52:56 GMT

Tinubu zai tafi ziyarar ƙasashe 3

Published: 13th, August 2025 GMT

Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wannan Alhamis din zai bar Abuja domin fita ziyarar aiki a ƙasashen Japan da Brazil, kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ta tabbatar.

Sai dai gabanin isa ƙasashen biyu, Tinubu zai soma yada zango a birnin Dubai na Hadaddiyar Daular Larabawa sannan daga bisani ya ƙarasa Japan.

An naɗa sabon Sarkin Alkaleri a Bauchi Rashin aiwatar da doka na bai wa masu laifi ƙwarin guiwa — Ɗan majalisar Gombe

A yayin da shugaban yake Japan, zai halarci taron Tokyo International Conference on African Development (TICAD9) karo na tara  a birnin Yokohama daga ranar 20 zuwa 22 ga watan Agusta.

Taken taron na bana shi ne “Haɗa Hannu da Afirka Wajen Ƙirƙirar Sabbin Hanyoyin Ci Gaba”, inda za a tattauna kan yadda za a sauya yanayin tattalin arzikin nahiyar da inganta kasuwanci.

Haka kuma taron na TICAD9 zai mayar da hankali kan ƙarfafa zaman lafiya, tsaro, da daidaito.

Baya ga wannan taron, Shugaba Tinubu zai yi zama na musamman da wasu shugabanni, tare da ganawa da shugabannin manyan kamfanonin Japan da ke da jarin kasuwanci a Nijeriya.

TICAD, wanda gwamnatin Japan ta ƙaddamar tun 1993 tare da haɗin gwiwar Majalisar Ɗinkin Duniya (UN), da Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU), da kuma Bankin Duniya, ana gudanar da shi duk bayan shekara uku a tsakanin Japan da Afirka, inda karo na ƙarshe ya gudana a Tunisia a Agustan 2022.

Bayan kammala ziyarsa a Japan, Shugaba Tinubu zai wuce Brasília, babban birnin ƙasar Brazil, daga Lahadi 24 zuwa Litinin 25 ga watan Agusta, bisa gayyatar shugaban ƙasar Luiz Inacio Lula da Silva.

A Brazil, Shugaba Tinubu zai yi ganawa ta musamman da shugaban ƙasar, sannan ya halarci babban taron kasuwanci da ‘yan kasuwar Brazil.

Tawagarsa wadda ta ƙunshi ministoci da manyan jami’ai, za ta tattauna da mahukunta kan batutuwan haɗin gwiwa tare da sanya hannu kan yarjejeniyoyi da takardun fahimtar juna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Brazil

এছাড়াও পড়ুন:

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano October 10, 2025 Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi October 10, 2025 Manyan Labarai Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC  October 9, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
  • Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina