Aminiya:
2025-08-13@20:55:41 GMT

Tinubu zai tafi ziyarar ƙasashe 3

Published: 13th, August 2025 GMT

Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wannan Alhamis din zai bar Abuja domin fita ziyarar aiki a ƙasashen Japan da Brazil, kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ta tabbatar.

Sai dai gabanin isa ƙasashen biyu, Tinubu zai soma yada zango a birnin Dubai na Hadaddiyar Daular Larabawa sannan daga bisani ya ƙarasa Japan.

An naɗa sabon Sarkin Alkaleri a Bauchi Rashin aiwatar da doka na bai wa masu laifi ƙwarin guiwa — Ɗan majalisar Gombe

A yayin da shugaban yake Japan, zai halarci taron Tokyo International Conference on African Development (TICAD9) karo na tara  a birnin Yokohama daga ranar 20 zuwa 22 ga watan Agusta.

Taken taron na bana shi ne “Haɗa Hannu da Afirka Wajen Ƙirƙirar Sabbin Hanyoyin Ci Gaba”, inda za a tattauna kan yadda za a sauya yanayin tattalin arzikin nahiyar da inganta kasuwanci.

Haka kuma taron na TICAD9 zai mayar da hankali kan ƙarfafa zaman lafiya, tsaro, da daidaito.

Baya ga wannan taron, Shugaba Tinubu zai yi zama na musamman da wasu shugabanni, tare da ganawa da shugabannin manyan kamfanonin Japan da ke da jarin kasuwanci a Nijeriya.

TICAD, wanda gwamnatin Japan ta ƙaddamar tun 1993 tare da haɗin gwiwar Majalisar Ɗinkin Duniya (UN), da Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU), da kuma Bankin Duniya, ana gudanar da shi duk bayan shekara uku a tsakanin Japan da Afirka, inda karo na ƙarshe ya gudana a Tunisia a Agustan 2022.

Bayan kammala ziyarsa a Japan, Shugaba Tinubu zai wuce Brasília, babban birnin ƙasar Brazil, daga Lahadi 24 zuwa Litinin 25 ga watan Agusta, bisa gayyatar shugaban ƙasar Luiz Inacio Lula da Silva.

A Brazil, Shugaba Tinubu zai yi ganawa ta musamman da shugaban ƙasar, sannan ya halarci babban taron kasuwanci da ‘yan kasuwar Brazil.

Tawagarsa wadda ta ƙunshi ministoci da manyan jami’ai, za ta tattauna da mahukunta kan batutuwan haɗin gwiwa tare da sanya hannu kan yarjejeniyoyi da takardun fahimtar juna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Brazil

এছাড়াও পড়ুন:

Mahukuntan Iraki Sun Bayyana Cewa: Akwai Yiwuwar Masu Ziyarar Arba’een Na Imam Husaini {a.s} Zasu Zarce Miliyan 4

Birnin Karbala mai tsarki na sa ran karbar bakwancin masu ziyara sama da miliyan 4 daga kasashen ketare domin gudanar da juyayin Arbaeen

Jama’a masu dimbin yawa na tururuwa zuwa birnin Karbala mai tsarki daga Najaf domin halartar yuyayin ranar Arbaeen a cikin tsauraran matakan tsaro da na hidima.

Wakilin Al-Alam da ke kan titin Karbala Mo’ataz Al-Aboudi ya ruwaito cewa: Ana ci gaba da zirga-zirgar masu ziyarar Arbaeen lami lafiya duk kuwa da tsananin zafi a kan hanyoyin da ke kan hanyar zuwa Karbala.

Wakilin na Al-Alam ya bayyana cewa: Birnin Karbala mai tsarki yana sa ran halartar masu ziyara sama da miliyan 4 daga wajen kasar Iraki, a cewar gwamnan Karbala Jassim Al-Khattabi. Ya yi nuni da cewa adadin masu halartar taron na iya zarce wannan adadin, domin mashigar kan iyaka da filayen tashi da saukar jiragen sama na ganin dimbin masu ziyara da ke shiga Iraki.

Wakilin Al-Alam ya bayyana cewa: Filin jirgin saman Najaf ya sanar da karbar jirage sama da 150 daga sassa daban-daban na duniya dauke da masu ziyarar Imam Husaini {a.s}.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Mamayar Isra’ila Sun kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Yankunan Zirin Gaza August 11, 2025 Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Gudanar Da Zaman Taro Kan Aniyar ‘Yan Sahayoniyya Kan Gaza August 11, 2025 Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza August 11, 2025 Israila Ta Kashe ‘Yan Jarida 4 A Harin Da Ta Kai Kan Tantinsu A Gaza August 11, 2025 Iran: Ba a yanke wani abu game da tattaunawa da Washington ba August 11, 2025 Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza August 11, 2025 Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari August 11, 2025 Chadi: An Daure Wani Dan Adawa Shekaru 20 A Gidan Kaso Da tara August 10, 2025 Dangantaka Tsakanin Iran da Saudiya Yana Taimakawa Zaman Lafiya A yankin August 10, 2025 Iran Zata Hana Amurka Samar da Hanya A yankin Caucasus Ko Rasha Bata taimaka ba August 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa
  • Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su
  • Iran: Janar Hatami ya karbi bakuncin babban hafsan hafsoshin sojin Afirka ta kudu
  • Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Mata Da Matasa
  • Mahukuntan Iraki Sun Bayyana Cewa: Akwai Yiwuwar Masu Ziyarar Arba’een Na Imam Husaini {a.s} Zasu Zarce Miliyan 4
  • Gwamna Bago Ya Kaddamar da Katafaren Kamfanin sarrafa Man Kade A Afirka.
  • Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan
  • Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari