Aminiya:
2025-08-12@17:00:05 GMT

Amurka da China sun dakatar da harajin da suka ƙaƙaba wa juna

Published: 12th, August 2025 GMT

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa ya rattaba hannu kan wata yarjejeniyar da za ta tsawaita dakatar da harajin da ya ƙaƙaba wa ƙasar China na tsawon kwanaki 90.

Trump ya sanar da hakan ne cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta na Truth Social, sa’o’i kaɗan kafin wa’adin farko da ya tsara ya ƙare.

Harin ’yan fashi: An rufe Federal Poly Bauchi Bauchi Mastering diverse trading strategies for market success

A ɗaya hannun, ma’aikatar kasuwanci ta ƙasar China ta kuma tabbatar da cewa ita ma ta dakatar da ƙarin haraji kan kayayyakin Amurka daga yanzu zuwa tsawon kwanaki 90, a matsayin martani.

Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya ruwaito cewa tun a watan Mayun da ya gabata, Washington da Beijing sun yi sa-in-sa dangane da harajin da ya kai kashi 145% kan kayayyakin China, da kuma kashi 125% kan kayayyakin Amurka.

Daga bisani, ɓangarorin biyu sun cimma matsaya wacce ta rage harajin da Amurka ta ƙaƙaba wa China zuwa kashi 30%, yayin da na kayayyakin Amurka a China ya ragu zuwa kashi 10%.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Haraji

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara

Sojoji sun samu nasarar kai wani gagarumin farmaki kan maboyar ’yan ta’addan da suka addabi manoma da mazauna wasu ƙauyuka a Jihar Zamfara da ke Arewa maso Yammacin Nijeriya.

Bayanai sun ce dakarun sojin na sama da ta ƙasa, waɗanda ke ƙarƙashin rundunar Operation Fasan Yamma da ke sintiri a Arewa maso Yamma domin kawar da masu tayar da ƙayar baya, sun hallaka sama da ’yan ta’adda 400 a yayin wannan samamen.

Za a gyara tarbiyar tubabbun ’yan daban Kano Direba ɗaya ya tsira a hatsarin tankokin dakon iskar gas a Zariya

Majiyoyi sun bayyana cewa ’yan ta’addan, waɗanda ke fakewa a dajin Makakkari tare da shugabanninsu daban-daban, sun dauki haramar kai hari kan wani ƙauye ne kafin sojojin su tari hanzarinsu.

Aminiya ta ruwaito cewa wannan farmakin na zuwa ne bayan zanga-zangar lumana da mazauna birnin Gusau suka gudanar a makon da ya gabata kan yadda matsalar tsaro ta ƙara tsananta a jihar.

Ana iya tuna cewa, a ranar Alhamis da ta gabata ce daruruwan mata, galibi tsofaffi da masu juna biyu daga ƙauyen Jimrawa, Kaura Namoda, suka fito kan titi domin nuna adawa da yadda matsalar rashin tsaron ta tsananta a bayan nan.

Mazauna dai sun yi ƙorafin cewa lalacewar hanyoyi a jihar na taimaka wa ’yan ta’adda wajen kai hare-hare, yayin da jami’an tsaro ke samun matsala wajen isa wuraren da ke fuskantar hare-hare  a kan kari.

Da yake ƙarin haske a ranar Litinin game da farmakin da sojoji suka kai a ranar Lahadi, mai magana da yawun rundunar sojin sama, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya ce bayan samun sahihan bayanan leƙen asiri, an gano kai-komon fiye da ‘yan ta’adda 400 suna shirin kai hari.

Ejodame ya ce: “An yi musu luguden wuta ta sama da ƙasa, inda aka kashe shugabannin ’yan ta’adda da dama da mabiyansu masu yawa.”

Ya ƙara da cewa, “haɗin kan da aka samu tsakanin sojojin sama da na ƙasa ne ya sanya wannan nasarar da muka samu ta zama ta musamman.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara
  • Ana Neman Daukar Karin Matakin Kawar Da Shingayen Dake Hana ‘Ya’ya Mata Zuwa Makaranta A Zamfara
  • Ma’aikatan shari’a 97 sun samu ƙarin girma a Borno
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • MDD za ta yi zaman gaggawa kan yunƙurin ƙwace Gaza
  • Tehran Times: Mai Yiwuwa Iran da Amurka su koma Tattaunawa
  • Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
  • ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki
  • Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika