Mutum 612 sun rasa matsuguni sanadiyyar ambaliya a Potiskum — NEMA
Published: 17th, August 2025 GMT
Mutum sama da 600 sun rasa matsuguni sanadiyyar wata mummunar ambaliya da ta afku a garin Potiskum da ke Jihar Yobe.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta bayyana cewa kimanin mutane 612 ne ta samarwa matsuguni bayan ambaliyar ruwa ta mamaye sama da gidaje 102 a garin Potiskum.
Wannan ambaliya ta afku ne a ranar Juma’a 15 ga watan Agusta shekara 2025.
NEMA tare da haɗin guiwar ma’aikatar ba da agaji ta jihar SEMA, sun killace mutanen a wani sansanin wucin gadi da aka kafa a makarantar firamare ta Sabon Gari, yayin da wasu ke samun mafaka a wurin ‘yan uwa da abokan arziki.
Ya zuwa yanzu, jami’an hukumomin NEMA da SEMA tare da haɗin guiwar Ƙungiyar Red Cross, IOM, ICRC da Cibiyar Kare Fararen Hula daga Rikici na ci gaba da aikin ceto da rarraba agajin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Jihar Yobe
এছাড়াও পড়ুন:
Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta samu nasara a wasan mako na 14 na Nigeria Premier Football League (NPFL), bayan da ta doke Ikorodu City da ci 2–1 a filin wasa na Muhammad Dikko, da ke birnin Katsina.
Wannan ita ce nasara ta uku da Pillars ta samu a kakar bana, cikin wasanninta 14, inda ta yi kunnen doki uku, sannan ta sha kashi shida.
’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun TuraiKafin wannan wasan, Kano Pillars ta yi wasanni takwas a jere ba tare da samun nasara ba.
Pillars ta zura kwallayenta ne ta hannun Rabiu Ali, wanda ya zura ta farko a minti na 3, sai Olakunle Alaka ya kara ta biyu a minti na 30.
A daidai minti na 45, kafin a je hutun rabin lokaci, Joseph Arumala ya rage tazara ga Ikorodu City.
Duk da wannan nasarar, Kano Pillars ta ci gaba da zama a matsayi na 20, inda take da maki 9 a ƙasan teburin gasar.
A wani labarin, ƙungiyar Katsina United ta samu nasarar doke Enyimba da ci 3–2 a birnin Ilorin, inda take buga wasanninta na gida bayan dakatar da ita daga yin wasa a filin gidan ta a Katsina.