Mutum 612 sun rasa matsuguni sanadiyyar ambaliya a Potiskum — NEMA
Published: 17th, August 2025 GMT
Mutum sama da 600 sun rasa matsuguni sanadiyyar wata mummunar ambaliya da ta afku a garin Potiskum da ke Jihar Yobe.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta bayyana cewa kimanin mutane 612 ne ta samarwa matsuguni bayan ambaliyar ruwa ta mamaye sama da gidaje 102 a garin Potiskum.
Wannan ambaliya ta afku ne a ranar Juma’a 15 ga watan Agusta shekara 2025.
NEMA tare da haɗin guiwar ma’aikatar ba da agaji ta jihar SEMA, sun killace mutanen a wani sansanin wucin gadi da aka kafa a makarantar firamare ta Sabon Gari, yayin da wasu ke samun mafaka a wurin ‘yan uwa da abokan arziki.
Ya zuwa yanzu, jami’an hukumomin NEMA da SEMA tare da haɗin guiwar Ƙungiyar Red Cross, IOM, ICRC da Cibiyar Kare Fararen Hula daga Rikici na ci gaba da aikin ceto da rarraba agajin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Jihar Yobe
এছাড়াও পড়ুন:
An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi
Jami’an tsaro sun kuɓutar da wasu fasinjoji 10 da aka yi garkuwa da su a hanyar Itobe – zuwa Ochadamu – Anyigba a Ƙaramar hukumar Ofu a Jihar Kogi.
Fasinjojin da aka kuɓutar an yi garkuwa da su ne a ranar 11 ga watan Agusta a ƙauyen Ugbakpedo da ke kan titin, lokacin da wata mota ta yi wa fasinjojin kwanton ɓauna.
Tinubu ya bar Abuja zuwa Japan da Brazil Matsalar ƙofa ta hana fasinjoji 58 hawa jirgin Abuja zuwa LandanJami’an tsaron da suka haɗa da: ’yan sanda da ’yan banga da mafarautan yankin sun bayyana cewa sun afkawa dajin da ke yankin kafin ceto matafiyan.
“A ranar 13 ga watan Agusta da misalin ƙarfe 4:30 na Asubahi ne yayin wani gagarumin farmaki tare da amfani da hayaƙi mai sa hawaye, masu garkuwa da mutanen suka yi watsi da waɗanda kama suka gudu.
“An ceto dukkan mutane 10 da aka yi garkuwan da su ba tare da sun samu rauni ba, kuma tuni aka haɗa su da iyalansu,” in ji wani rahoton tsaro kan lamarin.
Rahoton jami’an tsaro ya ƙara da cewa, ana ƙara tattara bayanan sirri da sa ido da kuma ganowa tare da yunkurin kama waɗanda ake zargin da suka tsere inda zargin masu garkuwa da mutane ne.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar (PPRO), SP William Aya ya tabbatar da ceto matafiya da aka yi garkuwa da su a ranar Juma’a a Lokoja.
Ya ce, an kuɓutar da matafiyan ne tare da haɗin gwiwa jami’an tsaro, tare da ‘yan banga da mafarauta wanda ya yi nasarar ceto waɗanda aka sace.