Mutum 612 sun rasa matsuguni sanadiyyar ambaliya a Potiskum — NEMA
Published: 17th, August 2025 GMT
Mutum sama da 600 sun rasa matsuguni sanadiyyar wata mummunar ambaliya da ta afku a garin Potiskum da ke Jihar Yobe.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta bayyana cewa kimanin mutane 612 ne ta samarwa matsuguni bayan ambaliyar ruwa ta mamaye sama da gidaje 102 a garin Potiskum.
Wannan ambaliya ta afku ne a ranar Juma’a 15 ga watan Agusta shekara 2025.
NEMA tare da haɗin guiwar ma’aikatar ba da agaji ta jihar SEMA, sun killace mutanen a wani sansanin wucin gadi da aka kafa a makarantar firamare ta Sabon Gari, yayin da wasu ke samun mafaka a wurin ‘yan uwa da abokan arziki.
Ya zuwa yanzu, jami’an hukumomin NEMA da SEMA tare da haɗin guiwar Ƙungiyar Red Cross, IOM, ICRC da Cibiyar Kare Fararen Hula daga Rikici na ci gaba da aikin ceto da rarraba agajin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Jihar Yobe
এছাড়াও পড়ুন:
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
Sanarwar ta kara da cewa, “mun yi farin cikin ganin cewar yan wasan kungiyoyin biyu da jami’an wasan duk sun bar filin wasan ba tare da samun wani rauni ba kuma jami’an tsaro suka yi musu rakiya, kungiyar ta kara da cewa an kama wasu da dama da ake zargi da hannu a rikicin tare da mika su ga hukumomin tsaro domin gudanar da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.
Kungiyar ta jaddada kudirinta na tabbatar da zaman lafiya da da’a, kungiyar ta jaddada cewa za ta ci gaba da tabbatar da ingancin wasan kamar yadda hukumar NPFL da hukumar kwallon kafar Najeriya NFF ta tanada, Pillars ta kuma yi kira ga magoya bayanta da su gudanar da ayyukansu cikin lumana tare da ci gaba da ba kungiyar goyon baya, amma kuma wani bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta ya nuna yan wasan 3SC da aka jikkata tareda raunuka a jikinsu.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA