Aminiya:
2025-10-13@15:50:01 GMT

APC ya lashe zaɓen cike gurbi a Zariya

Published: 17th, August 2025 GMT

An bayyana sakamakon zaɓen cike gurbi da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Zariya da kewaye, da kuma Mazabar Basawa da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, jihar Kaduna.

Zaɓen ya gudana cikin kwanciyar hankali ba tare da rahoton tashin hankali ba.

Isa Haruna Ihamo na APC ya yi nasara

A zaɓen da aka gudanar a Zariya, Isa Haruna Ihamo na jam’iyyar APC ne ya samu nasara da ƙuri’u 26,613.

Nuhu Sada Abdullahi na jam’iyyar SDP ya zo na biyu da ƙuri’u 5,721, yayin da Mahmud Abdullahi Wappa na PDP ya samu ƙuri’u 5,331.

Tun watan Ramadan muke cikin duhu — Al’ummar Jauro Jatau NNPP ta lashe zaɓen Bagwai/Shanono a Kano

Farfesa Balarabe Abdullahi, wanda ya bayyana sakamakon zaɓen, ya tabbatar da cewa Isa Haruna Ihamo ya cika dukkan sharuddan da ake buƙata don lashe zaɓen.

APC ta ƙara yin nasara a Mazaɓar Basawa

A Mazaɓar Basawa da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, Farfesa Nasiru Rabi’u ya bayyana jam’iyyar APC a matsayin wadda ta lashe zaɓen da ƙuri’u 10,926, sai PDP ke biye da ƙuri’u 5,499.

Zaɓe cikin kwanciyar hankali

Rahotanni sun tabbatar da cewa zaɓen ya gudana cikin lumana ba tare da wata hayaniya ko rikici ba, lamarin da ya kara tabbatar da sahihancin sakamakon.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: lashe zaɓen

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta

 

Rundunar ‘yansanda ta tabbatar da cewa ana gudanar da cikakken bincike domin gano ainihin musabbabin mutuwarta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tsaro Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara October 5, 2025 Tsaro Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ October 4, 2025 Tsaro Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina September 22, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako
  • Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta
  • Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya