APC ya lashe zaɓen cike gurbi a Zariya
Published: 17th, August 2025 GMT
An bayyana sakamakon zaɓen cike gurbi da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Zariya da kewaye, da kuma Mazabar Basawa da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, jihar Kaduna.
Zaɓen ya gudana cikin kwanciyar hankali ba tare da rahoton tashin hankali ba.
Isa Haruna Ihamo na APC ya yi nasaraA zaɓen da aka gudanar a Zariya, Isa Haruna Ihamo na jam’iyyar APC ne ya samu nasara da ƙuri’u 26,613.
Nuhu Sada Abdullahi na jam’iyyar SDP ya zo na biyu da ƙuri’u 5,721, yayin da Mahmud Abdullahi Wappa na PDP ya samu ƙuri’u 5,331.
Tun watan Ramadan muke cikin duhu — Al’ummar Jauro Jatau NNPP ta lashe zaɓen Bagwai/Shanono a KanoFarfesa Balarabe Abdullahi, wanda ya bayyana sakamakon zaɓen, ya tabbatar da cewa Isa Haruna Ihamo ya cika dukkan sharuddan da ake buƙata don lashe zaɓen.
APC ta ƙara yin nasara a Mazaɓar BasawaA Mazaɓar Basawa da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, Farfesa Nasiru Rabi’u ya bayyana jam’iyyar APC a matsayin wadda ta lashe zaɓen da ƙuri’u 10,926, sai PDP ke biye da ƙuri’u 5,499.
Zaɓe cikin kwanciyar hankaliRahotanni sun tabbatar da cewa zaɓen ya gudana cikin lumana ba tare da wata hayaniya ko rikici ba, lamarin da ya kara tabbatar da sahihancin sakamakon.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: lashe zaɓen
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta
Rundunar ‘yansanda ta tabbatar da cewa ana gudanar da cikakken bincike domin gano ainihin musabbabin mutuwarta.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA