Rashin aiwatar da doka na bai wa masu laifi ƙwarin guiwa — Ɗan majalisar Gombe
Published: 13th, August 2025 GMT
Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Gombe, mai wakiltar Nafada ta Kudu, Adamu A. Musa, ya zargi gwamnati da ‘yan majalisun jihar da kasa aiwatar da dokokin da suke zartarwa.
Ya ce akwai dokar da aka zartar shekaru takwas da suka gabata domin yaƙi da fyaɗe da cin zarafin mata da yara, amma har yanzu ba a aiwatar da ita ba.
A cewarsa, majalisa tana yin doka sannan ta tura wa gwamna ya sanya hannu, amma daga baya a bar ta kamar ba ta da amfani.
Ya yi gargaɗin cewa irin wannan sakaci yana ƙara wa masu aikata laifi ƙwarin guiwa kuma yana haifar da ƙaruwar manyan laifuka.
Ya ce da ana aiwatar da dokokin, da tuni an rage irin waɗannan laifuka, amma a maimakon haka, idan aka kai rahoton laifi, masu kuɗi suna ɗaukar lauyoyi su fito da su ba tare da an hukunta su ba.
Ya kawo misalin wata ɗaliba a Kano da ake zargin shugaban makarantarsu ya kashe ta, inda tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi alƙawarin aiwatar da hukuncin kisa amma bai yi hakan ba har ya sauka daga mulki.
Haka kuma ya nuna cewa babu wani gwamna a jihohin Arewa da ya taɓa aiwatar da hukuncin kisa ga masu aikata irin waɗannan manyan laifuka.
Sai dai, ya ce zai yi duk mai yiwuwa don ganin a fara aiwatar da dokokin a jihar nan gaba kaɗan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Majalisa a aiwatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
A zahiri, zamanin da kasashen yammacin duniya ke ba da umarni ga kasashe masu tasowa ya riga ya wuce. An taba bin tsare-tsaren da kasashen yamma suka tanada, amma ba a samu nasarar da aka sa ran samu ba, wannan sakamako ya sa kasashe masu tasowa daina amincewa da huldar kasa da kasa da kasashen yamma suka tsara. Sai dai, ko wace irin sabuwar dangantakar sassan kasa da kasa muke bukata a zamanin yau?
A matsayinta na daya daga cikin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta sha yin kira da a kafa sabon nau’in huldar kasa da kasa bisa tushen mutunta juna, da adalci, da hadin gwiwa don tabbatar da moriyar juna. Wannan tunani shi ma ya bayyana sarai a cikin babbar shawarar inganta jagorancin duniya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a watan jiya.
Yayin da ake kawo karshen tsohon zamanin da kasashen yammacin duniya ke taka rawa a matsayin masu ba da umarni a duniya, kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka da kasar Sin, za su kara kawo ci gaba mai inganci, da adalci, da daidaito ga duniya, yayin da suke kokarin aiwatar da wasu sabbin tunani, gami da raya su a kai a kai. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA