Aminiya:
2025-07-31@17:54:29 GMT

Ukraine ta cimma yarjejeniya da Amurka kan haƙar ma’adinai

Published: 27th, February 2025 GMT

Ukraine ta amince da wata yarjejeniya da Amurka kan haƙar ma’adinai da cinikayyar albarkatun ƙasa.

Ana sa ran sanar da yarjejeniyar a hukumance a yau Laraba, inda za a ba wa kamfanonin Amurka dama su shiga harkar haƙar ma’adinai a Ukraine, ciki har da man fetur da iskar gas.

Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N860 a Legas Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno

Bisa ga bayanai, Amurka za ta samu wani kaso mai yawa daga ribar da za a samu, wanda zai iya kai wa Dala biliyan 500.

Duk da cewa ba a bayyana batun tallafin tsaro a cikin yarjejeniyar ba, ministar shari’ar Ukraine, Olha Stefanishyna, ta ce akwai wasu muhimman batutuwa da Ukraine za ta amfana da su.

A ranar Juma’a mai zuwa ne shugaba Volodymyr Zelenskyy, zai tafi Amurka don ganawa da shugaba Donald Trump domin kammala yarjejeniyar.

Ukraine za ta riƙa saka kaso 50 na ribar da ta ke samu daga ma’adinanta a wata gidauniya ta haɗin gwiwa da Amurka, kuma wani ɓangare na kuɗin za a yi amfani da shi wajen sake gina ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ukraine yarjejeniya

এছাড়াও পড়ুন:

Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya reshen Jihar Benuwe, a ranar Alhamis, ta bayyana cewa aƙalla shanu 340 na mambobinta ne aka sace a cikin watan Yuli na 2025.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren ƙungiyar na jiha, Ibrahim Galma ya fitar kuma aka rabawa manema labarai a Makurdi.

Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa

A cewar sanarwar, lamarin ya faru ne a garin Agatu da wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma da ke Jihar Benuwe.

Galma ya kuma yi zargin cewa, ɓarayin shanu da ke afkawa jama’a a Ƙaramar hukumar Agatu sun faɗaɗa hare-harensu zuwa sassan Jihar Kogi.

“A ranar 19 ga Yuli, 2025 wasu da ake zargin ’yan ƙabilar unguwar Eguma ne a ƙaramar hukumar Agatu sun sace shanu 73 na wani Sale Abubakar (makiyayi Fulani), kuma har ya zuwa yanzu ba a ƙwato shanun ba.

“A ranar 21/7/2025 wani gungun masu aikata laifuka daga unguwar Agatu sun yi awon gaba da shanu 80 na Ardo Sarkin Fulanin Bagana, an yi awon gaba da shanun ne a Jihar Kogi, kusa da kan iyaka da ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe.

Ɓarayin sun kwashe shanun zuwa ƙauyukan Agatu. Daga baya kuma, an ƙwato shanu 30 daga cikin 80 a Agatu, inda ba a iya gano 50 ba.

“A ranar 24 ga Yuli, 2025 wasu miyagu matasa ‘yan garin Agatu sun yi awon gaba da wasu shanu 213 na Garah Mobaba, hakan kuma ya faru ne a kan iyaka tsakanin Jihar Kogi da Ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe, haka kuma lamarin na faruwa a wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma ta Jihar Benuwe, inda aka samu rahotannin sace-sacen shanu da kuma kashe-kashen makiyaya.”

Shanun mallakin Sale Abubakar (makiyayin Fulani), kuma har ya zuwa yanzu, ba a ƙwato shanun da aka sace ba.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine
  • Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki