Gwamna Malam Umar Namadi na jihar Jigawa ya bayyana harkar kiwon dabbobi a matsayin babbar harkar tattalin arziki ta biyu a jihar baya ga noma.

Ya bayyana haka ne yayin rantsar da kwamishina na farko na ma’aikatar ci gaban kiwon dabbobi da aka kafa kwanan nan, Farfesa Salim Abdurrahman Lawal, a zauren majalisar zartarwa na gidan gwamnati da ke Dutse.

A cewarsa, baya ga noma, kiwon dabbobi shi ne babban abin da mutanen jihar Jigawa suka sanya a gaba.

Malam Umar Namadi ya kara da cewa kafa wannan ma’aikata na cikin shirin gwamnati na bude manyan damarmaki da ke cikin wannan bangare.

“Mun dauki mataki na musamman domin ingantawa da bunkasa bangaren kiwon dabbobi. Mun yi hadin gwiwa da dama, mun yi tuntuba da dama, kuma nan gaba kadan za a fara ganin sakamakon wannan tuntuba. Bisa wannan dalili muka ga ya dace mu kafa ma’aikatar da za ta jagoranci wannan aiki gaba.”

Game da zaben kwamishina na farko, Gwamna Namadi ya bayyana kwarin gwiwa a kan kwarewar Farfesa Salim Abdurrahman.

“Mutumin da aka rantsar a matsayin kwamishina na kiwon dabbobi, kwararre ne kuma masanin a wannan fannin. Daga digirinsa na farko zuwa na biyu  har na uku (PhD), duk ya yi su ne akan ilimin dabbobi. Don haka babu wani da ya fi dacewa da wannan aiki fiye da Farfesa Salim.”

Yayin da yake taya Farfesa Salim Abdurrahman murna, Gwamnan ya tunasar da shi muhimmancin wannan mukami na farko da yake rike da shi, yana mai kira gare shi da ya yi aiki domin amfanin jama’ar jihar Jigawa.

“Ina sanar da kai cewa kana daf da kafa tarihi domin kai ne kwamishina na farko na wannan ma’aikata. Don haka idan ma’aikatar ta yi tasiri ga rayuwar mutanen jihar Jigawa, tarihi zai yi alfahari da kai”.

Namadi ya yi addu’ar samun nasarar wannan ma’aikata wajen inganta rayuwar al’umma a fadin jihar.

 

Usman Mohammed Zaria

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Kwamishina kwamishina na farko Farfesa Salim jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta samu nasara a wasan mako na 14 na Nigeria Premier Football League (NPFL), bayan da ta doke Ikorodu City da ci 2–1 a filin wasa na Muhammad Dikko, da ke birnin Katsina.

Wannan ita ce nasara ta uku da Pillars ta samu a kakar bana, cikin wasanninta 14, inda ta yi kunnen doki uku, sannan ta sha kashi shida.

’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai

Kafin wannan wasan, Kano Pillars ta yi wasanni takwas a jere ba tare da samun nasara ba.

Pillars ta zura kwallayenta ne ta hannun Rabiu Ali, wanda ya zura ta farko a minti na 3, sai Olakunle Alaka ya kara ta biyu a minti na 30.
A daidai minti na 45, kafin a je hutun rabin lokaci, Joseph Arumala ya rage tazara ga Ikorodu City.

Duk da wannan nasarar, Kano Pillars ta ci gaba da zama a matsayi na 20, inda take da maki 9 a ƙasan teburin gasar.

A wani labarin, ƙungiyar Katsina United ta samu nasarar doke Enyimba da ci 3–2 a birnin Ilorin, inda take buga wasanninta na gida bayan dakatar da ita daga yin wasa a filin gidan ta a Katsina.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • Gwamna Namadi Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 900 ga Majalisa
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin