A yayin ziyarar, Gwamna Lawal ya jajantawa iyalan waɗanda suka rasa ‘yan uwansu tare da tabbatar wa al’ummar yankin ƙudurinsa na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi.

 

A nasa jawabin, gwamnan ya yi kakkausar suka ga hare-haren da ’yan bindiga ke kai wa a baya-bayan nan, yana mai cewa da gangan maƙiya ke nufin waɗannan munanan ayyuka don yaɗa tsoro a tsakanin al’umma.

 

“Na ziyarci garin Banga ne domin jajanta wa jama’a game da harin da ‘yan bindiga suka kai a kwanakin baya.

 

“Lokacin da abin takaicin ya faru, na kasance ba na kusa, amma daga samun labarin, na umarci mataimakin gwamna da ya jagoranci wata babbar tawaga domin ziyarar jaje.

 

“A jiya ne na dawo Gusau bayan tafiya, kuma na ga ya dace na fifita ziyarar al’ummar da abin ya shafa a yau.

 

“Ina so in jaddada kudirin gwamnatina na ƙara ƙoƙari wajen yaƙi da ’yan bindiga.”

 

“Allah ya tona asirin waɗanda suke da hannu wajen kai waɗannan munanan hare-hare da kashe-kashen rashin hankali, ya kuma kunyata su. Ina kira ga kowa da kowa da ya dage da addu’a domin kawo ƙarshen duk wani nau’in ta’addanci a jiharmu mai albarka.”

 

Mai Martaba Sarkin Kauran Namoda, Dakta Sunusi Ahmad, a madadin jama’a, ya yaba wa ƙoƙarin Gwamna Lawal na ɗaukar matakan gaggawa kan matsalolin da suka shafi tsaro.

 

“Waɗannan ziyarce-ziyarcen abin yabo ne ga al’ummar da abin ya shafa da kuma ƙaramar hukumar Kauran Namoda, kuma muna godiya, Allah ya ci gaba da yi maka jagora.”

 

Gwamnan ya kuma yi alƙawarin inganta ababen more rayuwa kamar hanyoyin sadarwa, wutar lantarki, ruwan sha, da ayyukan wayar salula a cikin al’ummomin da abin ya shafa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa

Fitaccen malamin addinin Musulunci nan daga Jihar Bauchi, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya rasu.

Ɗansa, Sayyadi Ali Dahiru Usman Bauchi ne,  ya tabbatar wa Aminiya rasuwar malamin.

Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka

Ya ce sun karɓi wannan ƙaddara tare da gode wa Allah bisa rayuwar da malamin ya yi.

“Tabbas Sheikh ya koma ga Mahaliccinsa. Daga Allah muke, kuma gare Shi za mu koma,” in ji Sayyadi.

“Lokacin Sheikh ya yi. Mun gode wa Allah Maɗaukaki. Ya bai wa Sheikh tsawon rai, kuma rayuwarsa ta yi kyau. Alhamdulillah,” in ji shi.

Sayyadi, ya ce zuwa yanzu ba su yanke inda za a yi jana’izar malamin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin