NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe
Published: 14th, August 2025 GMT
Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) a Jihar Gombe ta ce ta lalata wata babbar gonar Tabar wiwi a Karamar Hukumar Kaltungo a jihar Gombe.
Hukumar ta kuma ce ta kama miyagun kwayoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira tsakanin watan Yuni zuwa Agustan 2025.
’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin NajeriyaKwamandan Hukumar a jihar, Mallam Maijama’a Muhammad ne ya bayyana hakan a yayin wata ziyarar kulla zumunci da ya kai wa Darakta-Janar na kafar yada labarai mallakar jihar Gombe (GMC), Ibrahim Isa.
Ya ce an kama mutum 69 maza da mata da suke kokarin shigar da miyagun kwayoyi cikin jihar a wasu lokuta.
Muhammad ya kuma ce hukumar na amfani da dabarun rage samarwa da rage bukatar miyagun kwayoyi, tare da kira ga karin hadin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki.
Daga nan sai ya gode wa gwamnatin Jihar bisa bayar da motocin aiki guda biyu da gyaran ofishin hukumar, da inganta cibiyar farfado da masu shan miyagun kwayoyi
A nasa jawabin, Daktan kafar yada labaran, Ibrahim Isa, ya tabbatar wa NDLEA da goyon bayan kafar ta GMC, ciki har da bayar da lokacin watsa shirye-shirye kyauta, tare da alkawarin ci gaba da yin aiki tare wajen yakar ta’ammali da miyagun kwayoyi a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: kwayoyi Tabar wiwi miyagun kwayoyi
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kundin tsarin mulki na hukumar sadarwa ta Najeriya (NCC) da asusun samar da ayukka na kasa da kasa (USPF), dukkanin su a karkashin ma’aikatar sadarwa, kirkire-kirkire da tattalin arziki na zamani.
A cikin wata sanarwa da Bayo Onanuga, mai baiwa shugaban kasa shawara kan yada labarai ya fitar, ya ce an nada Idris Olorunnimbe a matsayin shugaban hukumar NCC, yayin da Dr. Aminu Waida ya ci gaba da zama mataimakin shugaban zartarwa/Babban jami’in gudanarwa, mukamin da aka nada shi a watan Oktoban 2023 kuma majalisar dattawa ta tabbatar da shi a watan Nuwamba na wannan shekarar.
A baya Olorunnimbe ya yi aiki a hukumar kula da ayyukan yi na jihar Legas (LSETF), inda ya jagoranci kwamitin masu ruwa da tsaki da gudanar da mulki tare da jagorantar shirye-shiryen samar da ayyukan yi da samar da kasuwanci ga matasa.
Sauran mambobin hukumar NCC sun hada da Abraham Oshidami (Kwamishina, Ayukkan Fasaha), Rimini Makama (Kwamishiniyar Gudanarwa), Hajia Maryam Bayi (Kwamishinar kula da ma’aikata), Col. Abdulwahab Lawal (Rtd), Sanata Lekan Mustafa, Chris Okorie, Gimbiya Oforitsenere Emiko, da Sakataren Hukumar.
Ga USPF, Dokta Bosun Tijani, Ministan Sadarwa, Ƙirƙiri da Tattalin Arziki na Zamani, zai zama shugaba. Olorunnimbe kuma an nada mataimakin shugaba.
Sauran mambobin sun hada da Oshidami, Makama, Aliyu Edogi Aliyu (wakilin FMCIDE), Joseph B. Faluyi (Ma’aikatar Kudi ta Tarayya), Auwal Mohammed (Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsare ta Tarayya), Uzoma Dozie, Peter Bankole, Abayomi Anthony Okanlawon, Gafar Oluwasegun Quadri, da Sakataren USPF.
PR/Bello Wakili