Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-13@12:01:36 GMT

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato

Published: 13th, August 2025 GMT

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato

Wani sabon rikici ya barke a jihar Sokoto inda ‘yan bindiga sun kai hari a wani masallaci a kauyen Marnouna da ke karamar hukumar Wurno, inda suka kashe akalla mutum daya tare da yin awon gaba da wasu da ba a tantance adadinsu ba a lokacin da ake sallar isha.

 

Shugaban jam’iyyar APC reshen jihar Sokoto, Alhaji Isah Sadik Achida, wanda ya fito daga yankin ya tabbatar da faruwar harin inda ya jaddada cewa maharan sun kuma kashe shugaban kungiyar masu sayar da babura na yankin a yayin farmakin.

 

Achida ya ci gaba da cewa, kwana biyu kacal kafin harin masallacin, ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyuka biyu da ke makwabtaka da su, Gidan Taru da Kwargaba, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna garin tare da jaddada cewa ‘yan bindigar sun kuma kashe wani dan uwa tare da kama iyalansa baki daya.

 

A cewar shugaban jam’iyyar APC, ‘yan ta’addan na kokarin kafa sansani a yankin domin fadada ayyukansu.

 

Achida ya tabbatar wa mazauna jihar cewa gwamnatin jihar da jami’an tsaro suna bakin kokarinsu domin yakar matsalar.

 

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Sakkwato, ASP Abubakar Rufa’i, ya tabbatar wa gidan rediyon Najeriya faruwar lamarin inda ya ce a yanzu ‘yan fashin na kai hare-hare a lokutan damina domin kai hare-haren ba tare da an gano su ba.

 

NASIR MALALI

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: APC Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara

Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargin ’yan kungiyar asiri ne tare da kwato musu wasu abubuwa na bata gari a Ilorin.

 

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, Adetoun Ejinre-Adeyemi ya fitar, ya ce, ‘yan sandan da ke aiki bisa sahihiyar bayanan sirri daga majiyoyin tsaron al’umma, sun dauki wami mataki kan wani harin fashi da makami da ya afku a wani dakin kwanan dalibai da ke unguwar Eleko, Ilorin.

Sanarwar ta ce ba tare da bata lokaci ba jami’an ‘yan sanda da ‘yan banga, sun kai ga kama wasu maza biyu da ake zargi.

 

Ta ce wadanda ake zargin sun hada da Ishola Adeyemi, da Ismail Rafiu dukkansu na Ibadan, jihar Oyo.

 

A cewarsa yayin da ake yi musu tambayoyi na farko, wadanda ake zargin sun amsa cewa wani Qudus mai suna “Tiny”, memba ne na kungiyar Ido Cult Fraternity, ya gayyace su zuwa Ilorin don kawar da wani dan kungiyar asiri.

 

Ya yi nuni da cewa, a lokacin da harin nasu bai yi nasara ba, sai suka koma yin fashi a gidajen kwanan dalibai a yankin.

 

Ya yi bayanin cewa wadanda ake zargin, tare da baje kolin da aka kwato an mika su zuwa Sashen Yaki da Fashi, Sashen Binciken Laifukan Jiha (SCID), hedikwatar Jiha, don ci gaba da bincike da kuma gurfanar da su a gaban kotu.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto
  • Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara
  • Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.
  • EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Sakkwato Tambuwal kan zargin N189bn
  • An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato