Aminiya:
2025-10-13@15:50:00 GMT

Tinubu na amfani da EFCC ya muzguna wa ’yan adawa — Atiku

Published: 12th, August 2025 GMT

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin Bola Tinubu da amfani da Hukumar EFCC wajen yi wa masu adawa da ita barazana.

Saƙon da ɗan takarar shugaban ƙasa a Zaɓen 2023 ya wallafa wannan Talatar a shafinsa na X, na zuwa ne bayan tsare tsohon Gwamnan Sakkwato, Sanata Aminu Waziri Tambuwal da EFCCn ta yi.

Amurka da China sun dakatar da harajin da suka ƙaƙaba wa juna Harin ’yan fashi: An rufe Federal Poly Bauchi Bauchi

A cewar Wazirin Adamawa, “dalilin da EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Sakkwato, Sanata Aminu Waziri Tambuwal, shi ne saboda yana cikin jam’iyyar adawa ta haɗaka.

“Wannan yana ƙara nuna yadda gwamnatin Tinubu ke ci gaba da yaɗa manufofinta na musgunawa, tsoratarwa, da rusa ‘yan adawa.”

Ya ƙara da cewa, “A yau dai duk wanda yake da alaƙa da ‘yan adawa to za a zarge shi da cin hanci da rashawa.

“Kuma da zarar an tilasta musu komawa kan tsarin tafiyar siyasar Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu, sai ya zama kamar an gafarta musu zunubansu ne.”

Martanin PDP

Ita ma jam’iyyar PDP reshen Jihar Sakkwato ta soki tsarewar da aka yi wa tsohon gwamnan, tana bayyana lamarin a matsayin “tuggun siyasa.”

Mai magana da yawun jam’iyyar a jihar, Hassan Sahabi Sanyinnawal, ya bayyana shi a matsayin yunƙurin rufe bakin jam’iyyun adawa da tsoratar da su.

Rahotanni sun ce EFCC da ke da alhakin yaƙi ta masu yi wa tattalin arziki ta’annati ta tsare Tambuwal a Abuja ranar Litinin kan zargin cire naira biliyan 189 ba bisa ƙa’ida ba, abin da ya saɓa wa dokar haramta sama-da-faɗi da kuɗi ta 2022.

Sai dai wasu majiyoyi daga hukumar sun ce gayyata ce kawai aka yi masa domin ya yi ƙarin haske kan batun, ba kama shi ba.

Tambuwal wanda ya taɓa zama shugaban Majalisar Wakilan Nijeriya, ya fara siyasarsa a jam’iyyar APC kafin ya koma PDP, sannan daga bisani ya shiga jam’iyyar haɗaka ta ADC, wacce ta ɗaura ɗamarar karɓe mulki daga hannun APC a 2027.

A bayan nan wasu rahotanni sun bayyana cewa EFCC ta gayyaci tsohon Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai kuma tsohon gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, wanda ake sa ran zai amsa cikin mako ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aminu Waziri Tambuwal Atiku Abubakar

এছাড়াও পড়ুন:

Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa Maryam Sanda afuwa, wadda aka yanke wa hukuncin kisa a shekarar 2020 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello, ɗan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Alhaji Haliru Bello.

Maryam,’ mai shekara 37, ta shafe shekaru shida da watanni takwas a gidan yarin Suleja kafin yi mata afuwa.

Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro

Rahotanni sun nuna cewar an yi mata afuwar ne bayan yin nadama da aikata kyakkyawan halaye.

Iyayen Maryam sun roƙi gwamnati da ta sake ta saboda ’ya’yanta biyu da ta ke da alhakin kula da su, tare da alƙawarin sauya halayenta.

Shugaba Tinubu, ya kuma yi wa wasu mutane afuwa da suka haɗa da Manjo Janar Mamman Vatsa, Ken Saro-Wiwa, da kuma Sir Herbert Macaulay.

Gaba ɗaya mutane 175 ne shugaban ya yi musu afuwa, ciki har da masu manyan laifuka, tsoffin fursunoni, da waɗanda suka yi kyakkyawan tuba.

Wannan shi ne karon farko da Shugaba Tinubu ya yi amfani da ikon yafe laifi don tausaya wa waɗanda suka aikata laifuka tun bayan hawansa mulki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP