Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja, ya yaba wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan kama Abubakar Abba, jagoran kungiyar Mahmuda, daya daga cikin manyan kungiyoyin ta’addanci da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta yi a Najeriya.

 

An ce an kama shi ne a Wawa da ke karamar hukumar Borgu ta Jihar Neja inda aka kai shi Abuja domin ci gaba da bincike.

 

Gwamna Umar Bago ya bayyana matakin a matsayin nuni da irin jajircewar da shugaba Bola Ahmed Tinubu ke yi na tabbatar da tsaro da walwalar ‘yan Nijeriya.

 

Gwamnan wanda ya yi magana ta bakin babban sakataren yada labaran sa, Bologi Ibrahim, ya ce, “Eh gaskiya ne, zan iya tabbatar da cewa hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta kama shugaban kungiyar Mahmuda da ke daya daga cikin kungiyoyin ta’addanci a yammacin Afirka, Abubakar Abba, wanda jami’an tsaron farin kaya DSS suka kama shi da ransa.

 

“Wannan babbar nasara ce a gare mu a matsayinmu na jama’a da kuma gwamnati, kuma Shugaba Tinubu ya cancanci a yaba masa kan wannan labari mai ban sha’awa, yana mai jaddada cewa “Kamun Abba ya nuna cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jajirce wajen kawo karshen rashin tsaro da kuma inganta rayuwar ‘yan Nijeriya. In ji Gwamna Bago.

 

Gwamnan ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar Neja za ta ci gaba da hada kai da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro domin ganin an dakile ta’addanci a jihar Neja da Najeriya.

 

ALIYU LAWAL.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rasha A Shirye Take Ta Taimaka Wa Najeriya A Fada Da Ta’addanci

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta sanar da cewa kasar a shirye take ta taimaka wa tarayyar Najeriya a fadan da take yi da ta’addanci.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Rasha Maria Zakharova ce ta bayyana hakan, sannan kuma ta jinjinawa kokarin da gwamnatin ta Najeriya take yi a wannan fagen na kalubalantar masu wuce gona da iri.

Zakharova ta kuma ce, matsayar Rasha ba ta sauya ba akan yadda take kallon ta’addanci a matsayin barazana ga zaman lafiya na duniya.

Haka nan kuma ta ce, Rasha a shirye take ta bayar da taimako da kuma aiki tare da kungiyoyin kasa da kasa da cibiyoyin MDD da kuma tarayyar Afirka.

Dangane da Najeriya, Zakharova ta kara da cewa; Rasha a shirye take ta ci gaba da bai wa Najeriya taimako, kuma sojoji da jami’an tsaron kasar suna da kwarewa mai yawa da su ka samu a fagen fada da ta’addanci.”

Haka nan kuma ta yi ishara da yadda fararen hula da su ka hada mata da yara suke jin jiki matuka saboda ayyukan ta’addanci.

Kasar Najeriya dai tana fama da matsalolin tsaro daga kungiyoyin ta’addanci da su ka hada Bokoharam, Iswap da kuma barayin daji masu garkuwa da mutane.

A cikin kasa da mako daya an sace daliban makarantun arewacin kasar da dama, da hakan ya tilastawa mahukunta rufe makarantu a jihohi masu yawa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Palasdinawa Sun Karbi Gawawwakin Shahidai 15 Daga ‘Yan Mamaya November 27, 2025 Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon  Dake Takawa Makiya Birki November 27, 2025 Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa November 27, 2025 An Zabi Iran A Cikin Majalisar Zartarwa Ta Hukumar Yaki Da Makamai Masu Guba Ta Duniya CWC November 27, 2025 HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin November 27, 2025 Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta November 27, 2025 An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki November 27, 2025 Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan November 27, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza November 26, 2025 Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu. November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasha A Shirye Take Ta Taimaka Wa Najeriya A Fada Da Ta’addanci
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Hizbullah: Isra’ila na kuskure idan ta na tunanin kashe-kashen kwamandodinmu zai kawo karshen kungiyar