Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse
Published: 14th, August 2025 GMT
Al’ummar garin Talasse da ke Ƙaramar Hukumar Balanga a Jihar Gombe, sun ce sun gaji da rayuwa cikin duhu har na tsawon shekaru 19.
Sun kuma bayyana takaicinsu bayan tsayawar aikin wutar lantarki da ya tsaya.
Ba a ba mu dala 100,000 da gwamnati ta mana alƙawari ba — Super Falcons NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a GombeAikin, wanda ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Billiri da Balanga, Ali Isa JC, ya fara tun farkon wannan shekara, ya sanya al’ummar yankin farin ciki bayan an kafa turakun wuta da na’urorin taransifoma.
Sai dai cikin watanni biyu da suka gabata, aikin ya tsaya ba tare da wani bayani ba.
“Yan siyasa su kan zo da alƙawura a lokacin zaɓe, sannan su ɓace bayan sun yi nasara,” in ji Yakubu Ayuba, mazaunin Talasse.
Ya ce rashin wuta ya jawo durƙushewar kasuwanci da tattalin arziƙi a yankin, kuma hakan zai yi tasiri a zaɓen 2027.
Wani mai sana’ar ɗinki, Musa Adamu Galadima, ya ce: “Janerata ya fi ƙarfinmu. Na kori yaran da ke koyon sana’a saboda ba zan iya ɗaukar nauyinsu ba.”
Shi ma Sulaiman Idris, mai sayar da lemun kwalba, ya ce yana kashe kusan Naira 10,000 a rana wajen siyan ƙanƙara.
“Lokacin da aka kawo kayan aiki mun yi farin ciki, amma yanzu komai ya tsaya,” in ji shi.
Da aka tuntuɓi ɗan majalisar don jin ta bakinsa, Ali Isa JC, ya ce matsalar ta samo asali ne daga jinkirin sakin kuɗaɗen aikin daga Gwamnatin Tarayya, amma suna ƙoƙarin ganin aikin ya ci gaba.
A halin yanzu, gwamnatin Jihar Gombe ta fara aikin samar da wuta ta hanyar samar da ƙaramar madatsar ruwa da hasken rana a Dam ɗin Balanga, wanda zai iya samar da 620KW.
Duk da haka, jama’ar Talasse sun ce rashin wutar zai sa su ƙauracewa kaɗa ƙuri’a a zaɓen 2027.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Majalisa Rashin Wuta Wutar Lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
Al’ummomin dake garin Warwade da kewaye a karamar hukumar Dutse ta jihar Jigawa sun yi kira ga gwamnatin jihar da ta yashe madatsar ruwa ta Warwade wanda ta kasance daya daga cikin hanyar samun aikin dogaro da kai ga Mazauna yankin.
Wakilinmu Usman Mohammed Zaria ya ziyarci al’ummomin da ke zaune a kusa da mmadatsr ruwan wanda aka gina ta sama da shekaru hamsin da suka gabata.
Madatsar ruwan ta Warwade ta kasance hanyar samun sana’o’in dogaro da kai ga mazauna yankin, wadanda suke kamun kifi da noman rani domin samun na yau da kullum.
Malam Umar Sani, wanda masunci ne a Warwade, yace da abin da yake samu daga kamun kifi yake kula da iyalan shi da kuma sauran bukatun yau da kullum.
Yace ana samun ribar kimanin naira dubu goma zuwa ashirin a kowace rana daga siyar da kifin ga matafiya da kuma baki masu kai ziyara garin.
A don haka, Umar yayi kira ga gwamnatin jihar Jigawa da ta yi yashen madatsar ruwan saboda a samu karin kifaye da kuma ruwa da za a iya amfani da shi domin noman rani.
Shi ma a yayin tattaunawa da Dagacin Warwade, Malam Musa Ado, ya ce madatsar ruwan tana samar da ayyukan yi ga matasan yankin, tare da hana tafiya zuwa cirani a sauran yankunan kasar nan da sunan yin sana’o’i.
Ya ce matasan yankin suna gudanar da sana’ar kamun kifi da kuma nomar rani da ta damina.
Sai dai kuma, Malam Musa ya koka kan rashin samar da injinan noman rani da kuma Malaman gona kamar yadda ake yi a gwamnatocin baya.
Kazalika, yace a ‘yan kwanakin baya gwamnatin jihar Jigawa ta kai ziyara kauyen inda ta sanar da cewar Bankin duniya zai samar da wasu kudade ta hannun gwamnatin tarayya wanda za’a baiwa gwamnatocin jihohi domin yashewa tare da gina burtuloli da hanyoyin noman rani.
Bisa haka ne dagacin yayi kira ga gwamnatin jihar da ta fara yin garambawul a madatsar ruwan domin a baiwa mazauna yankunan damar amfani da shi.
A shekarun baya dai, gwamnatin jihar Jigawan ta samar da irin kifaye guda dubu Dari uku domin inganta samar da kifi a yankin.
Usman Mohammed Zaria