Aminiya:
2025-11-27@21:56:07 GMT

Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse

Published: 14th, August 2025 GMT

Al’ummar garin Talasse da ke Ƙaramar Hukumar Balanga a Jihar Gombe, sun ce sun gaji da rayuwa cikin duhu har na tsawon shekaru 19.

Sun kuma bayyana takaicinsu bayan tsayawar aikin wutar lantarki da ya tsaya.

Ba a ba mu dala 100,000 da gwamnati ta mana alƙawari ba — Super Falcons NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe

Aikin, wanda ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Billiri da Balanga, Ali Isa JC, ya fara tun farkon wannan shekara, ya sanya al’ummar yankin farin ciki bayan an kafa turakun wuta da na’urorin taransifoma.

Sai dai cikin watanni biyu da suka gabata, aikin ya tsaya ba tare da wani bayani ba.

“Yan siyasa su kan zo da alƙawura a lokacin zaɓe, sannan su ɓace bayan sun yi nasara,” in ji Yakubu Ayuba, mazaunin Talasse.

Ya ce rashin wuta ya jawo durƙushewar kasuwanci da tattalin arziƙi a yankin, kuma hakan zai yi tasiri a zaɓen 2027.

Wani mai sana’ar ɗinki, Musa Adamu Galadima, ya ce: “Janerata ya fi ƙarfinmu. Na kori yaran da ke koyon sana’a saboda ba zan iya ɗaukar nauyinsu ba.”

Shi ma Sulaiman Idris, mai sayar da lemun kwalba, ya ce yana kashe kusan Naira 10,000 a rana wajen siyan ƙanƙara.

“Lokacin da aka kawo kayan aiki mun yi farin ciki, amma yanzu komai ya tsaya,” in ji shi.

Da aka tuntuɓi ɗan majalisar don jin ta bakinsa, Ali Isa JC, ya ce matsalar ta samo asali ne daga jinkirin sakin kuɗaɗen aikin daga Gwamnatin Tarayya, amma suna ƙoƙarin ganin aikin ya ci gaba.

A halin yanzu, gwamnatin Jihar Gombe ta fara aikin samar da wuta ta hanyar samar da ƙaramar madatsar ruwa da hasken rana a Dam ɗin Balanga, wanda zai iya samar da 620KW.

Duk da haka, jama’ar Talasse sun ce rashin wutar zai sa su ƙauracewa kaɗa ƙuri’a a zaɓen 2027.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Majalisa Rashin Wuta Wutar Lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Bauchi, a matsayin babban rashi ga al’umma.

Gwamnan ya bayyana malamin a matsayin jagoran haɗin kai, zaman lafiya, da fahimtar juna tsakanin Musulmi da mabiya addinai daban-daban.

’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa

A cikin saƙon ta’aziyya da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Mukhtar Gidado, ya sanya wa hannu, gwamnan ya ce Gwamnatin Jihar Bauchi tana alhinin rasuwar malamin.

Dahiru Bauchi, ya rasu da safiyar ranar Alhamis, 27 ga watan Nuwamba, 2025 a Bauchi, yana da shekara 102.

Gwamnan, ya ce Sheikh Dahiru Bauchi babban malami ne na addinin Musulunci, mai imani, tawali’u da hikima.

A cewarsa ya sadaukar da rayuwarsa wajen yaɗa addinin Musulunci, koyar da Alƙur’ani, da kuma taimaka wa mutane wajen tarbiyya.

Marigayin, ya koyar da dubban ɗalibai da suka haddace Alƙur’ani tare da yaɗa addinin Musulunci a sassan nahiyar Afrika.

Gwamnan, ya ƙara da cewa gudunmawar da marigayin ya bayar a fannin tafsiri, fiqhu da tarihi sun taka muhimmiyar rawa wajen ɗora al’umma kan turbar tsira.

Har ila yau, ya ce Gwamnatin Jihar Bauchi za ta ci gaba da girmama marigayin ta hanyar tallafa wa makarantu da manufofin da ya gina, musamman a fannin ilimin addinin Musulunci, tarbiyya da ci gaban al’umma.

Ya yi addu’a rAllah ya gafarta masa kurakuransa, ya sanya shi aAljannatul Firdausi, ya kuma bai wa iyalansa, mabiyansa da ɗaukacin al’ummar Musulmi haƙurin rashinsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin
  • Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta
  • Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta
  • Mali: An Dakatar Da  Aikin Kafafen Watsa Labarun Faransa Biyu A Cikin Kasar Mali
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin
  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe