Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar
Published: 14th, August 2025 GMT
Sabuwar mai bada shawara kan harkokin lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya, Maryam Bukar-Hassan (Alhan_islam) ta bayyana cewa samar da dauwamammen zaman lafiya a duniya shi ne fatansu.
Maryam ta bayyana hakan ne a lokacin da babban jami’in kula da ayyukan jin ƙai na Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya, Mohammed Malick Fall, ke maraba da ita a ofishin majalisar da ke Abuja.
Mohammed ya jaddada muhimmancin samar da zaman lafiya, yana mai cewa zaman lafiya wani abu ne da ake buƙata don jin daɗin rayuwar ɗan Adam, kuma idan ba a same shi ba, ci gaban dimokuraɗiyya da kuma ’yancin ɗan Adam ba zai samu ba.
Ya bayyana damuwarsa kan yadda aka sake samun ɓullar tashe-tashen hankula a Nijeriya da ma duniya baki ɗaya, yana mai cewa hakan koma baya ne ga ci gaban da aka samu tun kafuwar MDD shekara 80 da suka gabata.
Da take nata jawabin Maryam Bukar Hassan ta ce, akwai buƙatar a samar da wani shiri na kawo sauyi wajen samar da zaman lafiya mai ɗorewa.
Har ila yau, Mohammed Fall ya yaba da yadda aka naɗa Maryam Bukar-Hassan a matsayin, ya ce hakan yazo a daidai lokacin da ya dace kuma mai mahimmanci, yana mai bayyana irin ƙarfin gwiwar da yake da shi akanta na za ta sauke nauyin da aka ɗora mata, mussaman wajen isa ga al’umma da matasa ta hanyoyin diflomasiya.
Yana mai cewa, “Ku ne muryar matasa, muryar jagorancin mata,” in ji shi. Ya kuma jaddada irin rawar da taka wajen tsara makomar neman zaman lafiya.
Ya kuma bayyana cewa, nauyin da ke kanta ya yi fice a Nijeriya har zuwa ayyukan da duniya ke yi. Duk da irin rawar da take takawa a duniya, Fall ya ba ta tabbacin goyon bayan Majalisar Ɗinkin Duniya.
Hakazalika Maryam Bukar-Hassan ya jaddada cewa, idan har ba zaman lafiya ba, yadda za a iya cimma muradun ci gaba mai ɗorewa (SDGs) kuma zai kasance mara amfani.
“Ba maganar talauci idan zaman lafiya da yin adalci sun tabbata,” in ji ta,
Ta kuma ƙara da cewar, tabbatar da yunƙurin zaman lafiya ta hanyar haɗa harsunan asalin ƙabilu da al’adu na gargajiya ne fatanmu dole mu haɗa da harshen Ingilishi,” in ji ta.
Idan har muna son mu kai ga cimma nasara dole ne, mu komo hanyar yadda da al’ummominmu suka tsara. Wannan hanya na nufin tabbatar da gina zaman lafiya mai ɗorewa, musamman a yankunan da asalin al’adu ke taka muhimmiyar rawa a cikin zamantakewa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Ɗinkin Duniya Zaman lafiya Maryam Bukar Hassan zaman lafiya mai ɗorewa
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
A cewarta, shirin ya taimaka wajen noman shinkafa da ta kai kimanin tan 99,452, wacce kuma kudinta ya kai kimanin Naira biliyan 13.527 tare kuma da noman rogo da ya kai kimanin tan 87,237, wanda kudinsa ya kai Naira biliyan 3.925, musamman domin a kara samar da wadataccen abinci da kuma kara bunkasa fannin tattalin arzikin jihar.
Sai dai, ta bayyana cewa; har yanzu a jihar ba a samar da wani cikakken tsari a hukumance ba, a kan tsarin na shirin na CAF wanda hakan ke haifar wa da shirin koma baya a jihar.
Ta yi kira ga sauran masu ruwa da tsaki a fannin bunkasa aikin noma, domin samun riba a jihar da su bayar da hadin kai wajen shiga cikin tsarin na CAF, musamman a bangaren noman shinkafa da rogo da sauran amfanin gona.
Kazalika, ta bukaci mahukunta a jihar da su samar da tsari a hukumance, musamman na dogon zango domin ci gaba da samar da wadataccen abinci a fadin jihar baki-daya.
Shi ma a nasa bangaren, jami’in shirin na jihar; Dakta Emmanuel Igbaukum ya bayyana cewa, masu ruwa da tsaki a jihar, sun nuna sha’awarsu ta shiga cikin shirin tare kuma da sanya shi a cikin tsarin jihar na samar da abinci mai gina jiki.
Ya kara da cewa, shirin zai kuma taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin aikin noma na jihar baki-daya.
A nata jawabin, Babbar Sakatariya a ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci, Pharm. Elijah ta bayar da tabbacin cewa; gwamnatin jihar za ta bayar da kason kudi a kan lokaci tare kuma da yin rangwame wajen sayen kayan aikin noma cikin rahusa.
Ta bayyana cewa, gudunmawar shirin na IFAD ya taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin tattalin arziki da kuma fannin aikin noma na jihar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA