Tun watan Ramadan muke cikin duhu — Al’ummar Jauro Jatau
Published: 17th, August 2025 GMT
Al’ummar unguwar Jauro Jatau da ke kan hanyar Bypass a Ƙaramar Hukumar Akko, Jihar Gombe, sun koka kan dogon lokacin da suka shafe ba tare da samun wutar lantarki ba.
Sun roƙi gwamnati, ’yan siyasa da masu hannu da shuni da su kawo musu ɗauki cikin gaggawa.
Tun a watan RamadanAl’ummar sun bayyana cewa tun watan azumin Ramadan da ya gabata suke cikin duhu, sakamakon ƙonewar transforma da ke yankin, lamarin da ya bar su cikin ƙunci har tsawon watanni, da ke shafar rayuwar su ta yau da kullum.
Wani daga cikin mazauna yankin, Muhammad Idris Gargajiga, ya bayyana cewa duk lokacin da suka kai ƙorafi ana gaya musu cewa yankin ba shi da rumfar zaɓe, abin da ya kira da rashin adalci.
Sarkin Zuru ya rasu yana da shekara 81 NNPP ta lashe zaɓen Bagwai/Shanono a Kano“Mafi yawanmu, kusan kashi 90 bisa 100, mun fito ne daga cikin babban birnin Gombe muka zauna a nan. Amma har yanzu ana tauye mana kallon-kallon ba ‘yan asalin yankin ba,” in ji Idris.
Ya sake yin kira ga gwamnati da masu hannu da shuni da kuma ’yan siyasa da su dubi halin da suke ciki, su samar da transformer domin dawo da wutar lantarki.
Kasuwanci da walwala sun tsaya cikAl’ummar sun ce rashin wutar ya haifar da tsaiko a harkokin kasuwanci da walwala, tare da shafar rayuwar su ta yau da kullum. Sun bukaci hukumomi su gaggauta ɗaukar mataki domin dawo da wutar yankin.
JED ba ta amsa baWakilinmu ya yi ƙoƙarin tuntubar hukumar samar da hasken wutar lantarki ta Jos Electricity Distribution Company (JED), wadda ke da alhakin samar da wuta a yankin, amma hakan ya ci tura.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Gina Asibitin Dabbobi A Jihar Kwara
Ministan Ma’aikatar Kula da Kiwon Dabbobi, Alhaji Idi Mukhtar Maiha, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta amince da gina sabon asibitin dabbobi, da cibiyar ajiye dabbobi, tare da samar da allurar rigakafi a Jihar Kwara.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin gabatar da sakamakon nazarin taswirar fadin jihar(Geospatial Mapping) da aka gudanar a Ilori babban birnin Jihar Kwara.
Da yake wakiltar Ministan, Richard Mbaram ya bayyana wannan shiri a matsayin babbar nasara a tarihi wajen samo mafita ta dindindin ga rikicin manoma da makiyaya a ƙasar nan.
Ya ce aikin na daga cikin tsare-tsaren Shirin Sauya Hanyar Kiwo na Kasa (National Livestock Transformation Plan) na tsawon shekaru goma (2019-2028) wanda ya mayar da hankali kan gyara harkar kiwo a Najeriya.
A nasa jawabin, Kwamishinan Ƙasa na L-Press, Dr. Sanusi Abubakar, ya yaba wa Jihar Kwara bisa zuba jari a bangaren ci gaban kiwo.
Ya yi alkawarin ci gaba da bai wa gwamnatin jihar goyon baya domin cimma sabon tsari a harkar kiwo.
Shi ma Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, wanda Mai ba shi Shawara na Musamman Alhaji Sa’adu Salahudeen, ya wakilta, ya yaba wa cibiyar cike ta Jami’ar Bayero Kano bisa jajircewa da ƙwarewar da suka nuna a duk tsawon aikin.
Ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta aiwatar da sakamakon binciken ba tare da kaucewa daga abin da aka gano ba.
Gwamna AbdulRazaq ya yi kira ga sarakuna, abokan hulda, hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki da su hada hannu da gwamnati wajen aiwatar da shawarwarin da binciken ya bayar.
Tun da farko a jawabinsa, Darakta a Cibiyar Harkar Noma ta Jami’ar Bayero da ke Kano, Farfesa Sanusi Muhammed, ya bayyana cewa binciken ya samar da wani dandali mai inganci don tsara ayyuka, kai agaji, da ƙirƙirar manufofi a bangaren kiwo.
Farfesa Muhammed ya yi kira ga gwamnati da ta yi amfani da bayanan taswirar wajen gyaran ruwan sha na dabbobi da ƙirƙirar tsarin samar da ruwa mai jure canjin yanayi.
ALI MUHAMMAD RABIU