Aminiya:
2025-10-13@18:07:07 GMT

Tun watan Ramadan muke cikin duhu — Al’ummar Jauro Jatau

Published: 17th, August 2025 GMT

Al’ummar unguwar Jauro Jatau da ke kan hanyar Bypass a Ƙaramar Hukumar Akko, Jihar Gombe, sun koka kan dogon lokacin da suka shafe ba tare da samun wutar lantarki ba.

Sun roƙi gwamnati, ’yan siyasa da masu hannu da shuni da su kawo musu ɗauki cikin gaggawa.

Tun a watan Ramadan

Al’ummar sun bayyana cewa tun watan azumin Ramadan da ya gabata suke cikin duhu, sakamakon ƙonewar transforma da ke yankin, lamarin da ya bar su cikin ƙunci har tsawon watanni, da ke shafar rayuwar su ta yau da kullum.

Wani daga cikin mazauna yankin, Muhammad Idris Gargajiga, ya bayyana cewa duk lokacin da suka kai ƙorafi ana gaya musu cewa yankin ba shi da rumfar zaɓe, abin da ya kira da rashin adalci.

Sarkin Zuru ya rasu yana da shekara 81 NNPP ta lashe zaɓen Bagwai/Shanono a Kano

“Mafi yawanmu, kusan kashi 90 bisa 100, mun fito ne daga cikin babban birnin Gombe muka zauna a nan. Amma har yanzu ana tauye mana kallon-kallon ba ‘yan asalin yankin ba,” in ji Idris.

Ya sake yin kira ga gwamnati da masu hannu da shuni da kuma ’yan siyasa da su dubi halin da suke ciki, su samar da transformer domin dawo da wutar lantarki.

Kasuwanci da walwala sun tsaya cik

Al’ummar sun ce rashin wutar ya haifar da tsaiko a harkokin kasuwanci da walwala, tare da shafar rayuwar su ta yau da kullum. Sun bukaci hukumomi su gaggauta ɗaukar mataki domin dawo da wutar yankin.

JED ba ta amsa ba

Wakilinmu ya yi ƙoƙarin tuntubar hukumar samar da hasken wutar lantarki ta Jos Electricity Distribution Company (JED), wadda ke da alhakin samar da wuta a yankin, amma hakan ya ci tura.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya tafi birnin Rome na Ƙasar Italiya, domin halartar taron shugabannin ƙasashe kan sha’anin tsaro.

Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin labarai, Bayo Onanuga, ya ce za a fara taron ne a ranar 14 ga watan Oktoba, kuma zai mayar da hankali kan matsalar tsaro da ke addabar yankin Yammacin Afirka.

’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina

Taron na ‘Aqaba Process’ an kafa shi ne a shekarar 2015 ta hannun Sarki Abdullah II na Ƙasar Jordan, kuma ana gudanar da shi tare da haɗin gwiwar Jordan da ƙasar Italiya.

Taron na nufin tattauna hanyoyin yaƙi da ta’addanci da kuma magance matsalolin tsaro da ke adabbar ƙasashe daban-daban, musamman a yankin Yammacin Afirka.

Taron zai haɗa shugabannin ƙasashe na Afirka, jami’an leƙen asiri da na tsaro, da wakilan ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na ƙungiyoyin fararen hula, domin tattauna yadda za a magance matsalolin tsaro da ke addabar yankin.

Za a tattauna kan yadda ƙungiyoyin ta’addanci ke yaɗuwa a Yammacin Afirka, alaƙa tsakanin masu laifi da ’yan ta’adda, da kuma alaƙar da ke tsakanin ta’addanci a yankin Sahel.

Hakazalika, za a tattauna yadda za a daƙile yaɗuwar aƙidar ta’addanci a Intanet da kuma lalata hanyoyin sadarwar da ’yan ta’adda ke amfani da su wajen yaɗa ra’ayoyinsu da ɗaukar sababbin mabiya.

Shugaba Tinubu zai kuma tattauna da wasu shugabannin ƙasashe don neman hanyoyin daƙile matsalar tsaro da ke addabar yankin.

Tinubu ya samu rakiyar Ministan Harkokin Waje, Ambasada Bianca Odumegwu–Ojukwu; Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar.

Sauran sun haɗa daMai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu; Darakta-Janar na Hukumar Leƙen Asiri ta Ƙasa (NIA), Ambasada Mohammed Mohammed; da wasu manyan jami’an gwamnati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
  • Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya