Sahun farko na Alhazan Najeriya zai tashi zuwa kasa mai tsarki a ranar 9 ga watan Mayun 2025.

Hakan na kunshe ne a cikin bayanin bayan taro da Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON, ta yi da Shugabannin Hukomomin Kula da Jin Daɗin Alhazai na Jihohi a  ranar 22 ga watan Afrilun 2025.

Manufar taron ita ce tantance matakin shirin da kowace Hukumar Alhazai ta Jiha ta kai.

Wata sanarwa da mataimakiyar daraktar watsa labarai ta hukumar NAHCON, Fatima Sanda Usara ta fitar, ta ce shugaban hukumar, Farfesa Abdullah Saleh Usman, ya tunatar da mahalarta taron cewa harkar Hajji na cikin matakin karshe na shirye-shirye kafin fara aikin Hajjin shekarar 2025.

Ya bukaci jihohi da su sanar da NAHCON matsayin da suka kai wajen samar da biza, rigakafi, sayen jakunkuna da sauran batutuwa  da suka jibancu aikin hajji.

A yayin taron, Kwamishinan Ayyuka na NAHCON, Prince Anofiu Elegushi, ya bayyana cewa kamfanin Air Peace  zai yi jigilar alhazai 5,128 daga jihohin Abia, Akwa Ibom, Anambra, Rundunar Sojoji, Bayelsa, Benue, Borno, Cross River, Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, Imo, Kogi, Ondo, Rivers, da Taraba.

Yayin da kamfanin FlyNas zai dauki alhazai 12,506 daga Birnin Tarayya Abuja, Kebbi, Legas, Ogun, Osun, Sokoto da Zamfara. Kamfanin na FlyNas ya ware jirage tara domin gudanar da wannan aikin.

Sai kamfanin Max Air da zai dauki alhazai daga jihohin Bauchi, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kwara, Oyo da Filato.

Kamfanin na Max Air ya yi alkawarin kammala jigilar alhazai  15,203 zuwa ranar 24 ga Mayu, inda zai yi amfani da jirage biyu,  jirgin B747 mai daukar mutum 400, da wani mai daukar mutum 560.

Haka zalika, kamfanin Umza zai yi jigilar alhazai 10,163 daga jihohin Kaduna, Adamawa, Nasarawa, Neja da Yobe. Shi kuma zai yi amfani da jiragin B747 mai daukar mutum 477 da B777 mai daukar mutum 310.

Wadanda kamfanonin jiragen sama 4 za su yi jigilar alhazan Hajjin 2025 su 43,000.

Kwamishinan Tsare-tsare, Bincike, Kididdiga, Labarai da Ayyukan Laburare (PRSILS), Farfesa Abubakar Yagawal, ya bayyana wa mahalarta taron irin shirin da hukumar ta yi dangane da samar da asibitoci a Makka da Madina, rabon kati na Yellow Card ga jihohi, tare da tunatar da su da su guji yi wa mata masu ciki rijistar  aikin hajji.

Sanarwar ta kara da cewa yayin da aka cimma matsaya cewa ranar 9 ga Mayu za a fara tashi, ana kuma sa ran kammala jigilar a ranar 24 ga watan Mayu.

Har ila yau, sanarwar ta ce za a fara dawowa daga kasar mai tsarki a ranar 13 ga watan Yuni zuwa 2 ga watan Yuli, idan Allah ya yarda.

 

 

Safiyah Abdulkadir 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigilar Alhazai mai daukar mutum

এছাড়াও পড়ুন:

Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya
  • Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242