Aminiya:
2025-10-13@17:48:31 GMT

Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki

Published: 13th, August 2025 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Kano, ta dakatar da Shugaban Ƙaramar Hukumar Rano, Muhammad Nazir Yau, na tsawon wata uku domin gudanar da bincike kan zargin yin amfani da kujerarsa ba bisa ƙa’ida ba.

Kansilolinsa sun zarge shi da karkatar da kayayyaki da kuma almundahana wajen tafiyar da dukiyar jama’a.

Kullum a Kamaru muke kwana, mu yini a Najeriya – Mazauna ƙauyen Borno Lafiyar Tinubu kalau – Soludo

An yanke wannan hukunci ne bayan majalisar ta karɓi rahoto daga kwamitin karɓar koke-koke na jama’a, wanda shugaban marasa rinjaye na majalisar, Hussaini Lawan Cediyar Yangurasa, ya jagoranta a zaman ranar Laraba.

Majalisar ta kuma umarci ma’aikatar ƙananan hukumomi da harkokin masarautu ta jihar da ta bai wa mataimakin shugaban ƙaramar hukumar damar riƙon muƙamin shugaban har sai an kammala bincike.

A cewar rahoton, an zargi Yau da haifar da rigima tsakanin shugabannin siyasa da kansiloli, bayar da kayayyakin gwamnati ga magoya bayansa, rabon takardun shiga makarantar Dangote da takin zamani ba tare da adalci ba.

Hakazalika, an zarge shi da sayar da takin gwamnati sama da farashin da aka amince da shi na Naira 20,000 ba tare da sanar da kansiloli ba.

Har ila yau akwai zarge-zarge da suka haɗa da rashin gaskiya wajen tafiyar da kuɗaɗen shiga daga kasuwanni da kuɗaɗen harajin dabbobi, sayar da rumfunan kasuwa ba tare da izini ba.

Sauran zarge-zargen sun haɗa da raina dattawan jam’iyya da sauran masu ruwa da tsaki, da kuma yin amfani da kuɗaɗen ƙaramar hukuma ba bisa ƙa’ida ba.

Kwamitin ya zauna da ɓangarorin biyu a ranar 11 ga watan Agusta, inda shugaban ya musanta wasu daga cikin zarge-zargen amma ya amince cewa ya ƙara Naira Naira 2,000 a kan farashin takin zamani da gwamnati ta amince da shi.

Bisa ga sashe na 55 na dokar ƙananan hukumomi ta shekarar 2006, kwamitin ya tabbatar da dakatar da shi domin gudanar da cikakken bincike.

Sannan ta umarci a miƙa dukkanin takardun kuɗi da na gudanarwa na ƙaramar hukumar cikin kwanaki bakwai.

A zaman majalisar na ranar Laraba, wanda kakakin majalisar Ismail Falgore ya jagoranta, majalisar ta amince da shawarwarin kwamitin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki Shugaban Ƙaramar Hukuma Zarge zarge zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Tawagar da ke karkashin jagorancin, Barry Andrews ta kuma ziyarci hedkwatar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), inda shugabanta, Mahmood Yakubu, ya yi gargadin cewa jinkirin da ‘yan majalisa ke yi wajen gyaran dokar zabe ta 2022 na iya kawo cikas ga shirye-shiryen gudanar da zabe a 2027.

 

Wakilan, wadanda suke Nijeriya tun kusan makonni uku domin nazarin matakin aiwatar da shawarwarin da ke cikin rahotonsu na bayan zaben 2023, sun kuma yi tattauna da babbar jam’iyyar adawa ta PDP.

 

Abbas, a cikin wata sanarwar da sakataren yada labaransa, Leke Bayeiwu, ya shaida wa tawagar EU cewa rahotanninta kan zabukan shekarar 2023 ana la’akari da su a cikin sauye-sauyen gyara dokar zabe da na dimokuradiyya da Majalisar dokoki ke gudanarwa.

 

Abbas ya ce, “Ina so in bayyana cewa shugabancin kasar nan karkashin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yana kokarin tabbatar da cewa mun inganta tsarin zabenmu, musamman game da abubuwan da masu saka ido na kasashen waje suka lura da su a lokacin zaben 2023.

 

“Mu a majalisar kasa ma mun kasance cikin aiki tukuru wajen tattara mafi yawan batutuwa da suka taso daga zaben 2023, domin mu ga yadda za mu iya magance su ta hanyar bin dokoki, domin zabenmu na gaba ya kasance mai inganci da amsuwa a idon duniya.”

 

Ya shaida wa tawagar cewa taron shugabannin majalisar dattawa da na majalisar wakilai da aka yi kwanan nan ya yanke shawarar warware batutuwan gyaran tsarin zabe cikin hanzari.

 

Ya bayyana cewa ra’ayin da yawa daga ‘yan majalisar kasa shi ne, gudanar da zabe a rana guda ba wai kawai zai kara inganci da gaskiya a gudanar da zaben kadai ba, har ma zai rage yawan kashe kudade na kusan kashi 40 cikin dari.

 

Ya ce, “Kamar gudanar da zabe a rana daya, wanda zai bayar da damar gudanar da zaben shugaban kasa da mambobin majalisar tarayya da gwamnonin jihohi da kuma ‘yan majalisar dokoki na jihohi duka a rana guda.

 

“A tunaninmu, zai taimaka wajen rage kashe kudaden gudanar da zabenmu har kashi 40 cikin ddari idan muka iya gudanar da zabukan cikin rana guda. Hakan zai kuma inganta gaskiya da karfafa aiki yadda ya kamata, musamman wajen fitowar masu kada kuri’a.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tambarin Dimokuradiyya 2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe October 10, 2025 Tambarin Dimokuradiyya ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu October 3, 2025 Tambarin Dimokuradiyya Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar October 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano
  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
  • ASUU ta tsunduma yajin aikin mako 2
  • Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina
  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
  • ASUU za ta fara yajin aikin mako 2 daga ranar Litinin
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano
  • Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha
  • Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya