Iran Ta Bukaci Mayar Da Martani Kan Aniyar Isra’ila Ta Mamaye Yankunan Kasashe Domin Kafa ‘Babbar Isra’ila’
Published: 14th, August 2025 GMT
Kasar Iran ta jaddada wajabcin daukar kwararan matakai na kasa da kasa don dakile muradun gwamnatin mamaya na mulkin mallaka
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Ismail Baqa’i ya yi Allah wadai da kalaman fira ministan gwamnatin ‘yan sahayoniyya da ake nema ruwa a jallo a kotun kasa da kasa ya yi dangane da abin da ake kira “Kafa kasar babban Isra’ila”.
A cikin wani rubutu da ya wallafa a safiyar yau Alhamis, Baqa’i ya yi ishara da yadda ake ci gaba da keta doka da kuma aikata munanan laifuka da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta ke tafkawa, musamman ma mamaye yankunan Falasdinawa da kisan kare dangi da ake ci gaba da yi a kan al’umma Falasdinu.
Baqa’i ya ci gaba da cewa: Amincewar da fira ministan gwamnatin ‘yan sahayoniyya ya yi na cewa yana da ”aiki na tarihi da na ruhi” don tabbatar da wannan muguwar tunani tun daga kogin Nilu har zuwa Fırat, wata shaida ce karara ta mulkin mallaka ta masu yanke shawarar wannan gwamnati ta miyagun al’umma da kuma kai hari kan ‘yantacciyar kasa mai ikon domin mamaye yankunan kasashensu, kuma wajibi ne a yi Allah wadai da wannan muguwar manufa ta tunanin mamaye yankunan kasashen musulmi daga babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da kungiyar hadin kan kasashen musulmi, da dukkanin gwamnatoci, a matsayin wannan furuci na cin zarafi da keta ƙa’idodi da manufofin Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya da dokokin dokokin ƙasa da ƙasa.”
Iran
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ya Bayyana Isra’ila A Matsayar ‘Yar Yaudara August 14, 2025 Hizbullahi Ta Yaba Wa Iran Kan Irin Gudumawarta Ga Lebanon Da Gwagwarmaya August 14, 2025 Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Fatali Da Batun Kafa Gwamnatin Hadaka A Kasar Sudan August 14, 2025 Larijani a Beirut: Iran A Shirye take ta taimaka ma Lebanon August 14, 2025 Masar ta yi Allawadai da furucin Netanyahu kan shirin kafa Isra’ila Babba August 14, 2025 Hamas ta aike da sakon jinjina ga al’ummar Yemen kan goyon bayan Gaza August 14, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 130 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 129 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 128 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 127 August 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: A Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Lokaci ya yi da za a amince da takunkumin da bai dace ba a matsayin laifi ga bil’adama
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya ce lokaci ya yi da za a amince da takunkumin bai daya da Amurka da kawayenta suka kakaba wa Iran a matsayin wani laifi na cin zarafin bil adama.
A cikin shafinsa na dandalin X, Araqchi ya bayyana cewa: “Gwamnatocin yammacin duniya a koyaushe suna da’awar cewa takunkumin zaman lafiya ne maimakon yakin zubar da jinni, amma gaskiyar tana bayyana wani labari na daban.”
Ya yi nuni da wani bincike na baya-bayan nan da aka buga a cikin jaridar The Lancet, wanda ya nuna cewa takunkumin bai-daya-musamman wanda Amurka ta kakabawa—na iya zama mai kisa kamar tashe-tashen hankula.
Ya kara da cewa; “Tun daga shekara ta 1970, sama da mutane 500,000 ne ke mutuwa a duk shekara sakamakon takunkumin da aka sanya musu, inda akasarin wadanda abin ya shafa yara ne da kuma tsofaffi.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Jaddada Kasancewar Iran Tare Da Kasar Lebanon Koda Yaushe August 13, 2025 Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin August 13, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida August 13, 2025 Wakilan Hamas sun isa Alkahira don shawarwarin tsagaita wuta a Gaza August 13, 2025 Iran: Amurka Da Isra’ila Ne Da Kansu Suka Bukaci Dakatar Da Bude Wuta August 13, 2025 Habasha: Madatsar ruwanmu amfanin dukkanin kasashen yankin ne August 13, 2025 Bankin Duniya Zai Kashe $300m Don Inganta Rayuwar ’Yan Gudun Hijira A Arewacin Nijeriya August 13, 2025 Nijeriya Da Isra’ila Na Kara Karfafa Alaka A Tsakaninsu August 13, 2025 Kasashe 27 Sun Bukaci Isara’ila Ta Kawo Karshen Hana Shigar Da Abinci A Gaza August 12, 2025 Iran: Duk Wani Sabon Hari, Zai Fuskanci Mummunan Martanin Soji August 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci