Aminiya:
2025-08-17@08:03:47 GMT

NNPP ta lashe zaɓen Bagwai/Shanono a Kano

Published: 17th, August 2025 GMT

Jam’iyyar NNPP wato New Nigeria Peoples Party, ta lashe zaɓen cike gurbi na majalisar dokokin tarayya da aka gudanar a ƙananan hukumomin Bagwai da Shanono da ke Jihar Kano.

Babban jami’in da ya tattara sakamakon zaɓen, Farfesa Hassan Adamu ne ya bayyana hakan da misalin ƙarfe 12:36 na daren Asabar wayewar gari Lahadi.

Farfesa Hassan Adamu Shitu, ya bayyana ɗan takarar jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaɓen da ƙuri’u 16,198, inda ya kayar da ɗan takarar jam’iyyar APC —All Progressives Congress — wanda ya samu ƙuri’u 5,347.

Dokta Ali Hassan Kiyawa na jam’iyyar NNPP shi ne ya yi nasara a kan Ahmad Muhammad Kadamu na jam’iyyar APC bayan zaɓen da aka gudanar a ranar Asabar

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Ahmed Maiyaki da Sadiq Mamman Legas a madadin gwamnatin jihar Kaduna sun ce ofishin babban lauyan gwamnati da kwamishinan shari’a zai yi nazari kan kalaman da kungiyar hadaka ta ADC ta yi tare da baiwa gwamnatin jihar shawara kan mataki na gaba.

Tun da farko a wani taron manema labarai, jam’iyyar African Democratic Congress da hadin gwiwarta sun zargi gwamnatin jihar Kaduna da daukar hayar ‘yan baranda sama da 4000 tare da cire naira miliyan 30 daga asusun kowace karamar hukuma domin kawo cikas ga zaben da ke tafe.Wannan shi ne bayanin da mataimakin shugaban jam’iyyar ADC na kasa reshen Arewa maso Yamma, Jafaru Ibrahim Sani da Shugaban Jam’iyyar na Jihar Kaduna Patrick Ambut.

A cewarsu, sun aika da koke ga INEC da hukumomin tsaro dangane da hakan.Wannan shi ne bayanin da mataimakin shugaban jam’iyyar ADC na kasa reshen Arewa maso Yamma, Jafaru Ibrahim Sani da Shugaban Jam’iyyar na Jihar Kaduna Patrick Ambut.

A cewarsu, sun aika da koke ga INEC da hukumomin tsaro dangane da hakan.ugaban jam’iyyar ADC na kasa reshen Arewa maso Yamma, Jafaru Ibrahim Sani da Shugaban Jam’iyyar na Jihar Kaduna Patrick Ambut.

A cewarsu, sun aika da koke ga INEC da hukumomin tsaro dangane da hakan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APC ta lashe zaɓen cike gurbi na Ghari/Tsanyawa a Kano
  • APC ta nemi INEC ta soke zaɓen cike gurbin Kano
  • Zaɓen cike gurbi: An samu ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a Zariya
  • APC ta buƙaci a soke zaɓen cike gurbi a Kano
  • An kama ’yan daba 288 yayin zaɓen cike gurbi a Kano
  • Zaɓen cike gurbi: An kama ’yan daba 100 a Bagwai — INEC
  • An kama shi da N25m na sayen kuri’u a zaɓen Kaduna
  • Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe
  • Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC