Aminiya:
2025-11-27@21:50:42 GMT

Zaɓen cike gurbi: An samu ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a Zariya

Published: 16th, August 2025 GMT

Aƙalla mutum 164,390 ake sa ran za su kaɗa ƙuri’a a zaɓen cike gurbi na ɗan majalisar dokokin Jihar Kaduna a mazaɓar Zariya da kewaye.

Sai dai yawancin masu zaɓe ba su fito ba.

APC ta buƙaci a soke zaɓen cike gurbi a Kano An kama ’yan daba 288 yayin zaɓen cike gurbi a Kano

Wakilinmu ya zagaya rumfunan zaɓe, inda ya gane wa idonsa yadda aikin zaɓen ke tafiya a hankali saboda matsalar na’urar tantancewa.

Malam Halliru Hamza, ya ce shi ma bai samu damar kaɗa ƙuri’a ba saboda na’urar taƙi ta tantance shi.

Ya ƙara da cewa mutane da dama ba su fito ba saboda yadda siyasa ke tafiya ba tare da ci gaba ba, sai tsadar rayuwa da rashin tsaro.

A gefe guda kuma, Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kaduna, Alhaji Ahmed Maiyaki, ya musanta zargin ‘yan adawa na cewa jam’iyyar APC ta shirya tafka maguɗi.

Ya ce hakan kawai alamar tsoro ne.

Kwamishinan ya ce APC ta yi aiki tuƙuru wajen neman goyon bayan jama’a, inda Gwamna Uba Sani da Kakakin Majalisar Wakilai na Tarayya, Abbas Tajudeen, suka jagoranci kamfen a wurare daban-daban ciki har da Zariya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zaɓen Cike Gurbi Zariya zaɓen cike gurbi

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Cutar amosanin jini wacce aka fi sani da cutar sikila na cigaba da barazana ga rayukan masu dauke da ita.

Wannan cuta na saka masu ita da ‘yan uwan su cikin halin ha’ula’i, a wasu lokutan ma tana haifar da rasa rayukan wasu dake dauke da ita.
Rahotannin Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) sun nuna cewa, kusan yara 300,000 ne ake haifa da cutar Sikila a duk shekara a fadin duniya, inda yankin Kudu da Sahara a Afirka ke dauke da kashi 75% na wannan yawan.
A Najeriya kadai, ana kiyasta cewa fiye da yara 150,000 ake haifa da cutar Sikila a kowace shekara — hakan ya sa Najeriya ke da mafi yawan masu fama da cutar Sikila a duniya.

NAJERIYA A YAU: Halin Da Shirin Samar Da Tsaro A Makarantun Najeriya Ke Ciki DAGA LARABA: Hanyoyin Da Suka Kamata A Bi Wajen Ceto Daliban Kebbi Da Aka Sace

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan cutar amosanin jini don gano yadda masu fama da ita ke ji a rayuwar su.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makaamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan
  • NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta