Kotun kasar Kanada ta ayyana APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci
Published: 15th, August 2025 GMT
Wata kotun tarayya a kasar Kanada ta ayyana manyan jam’iyyun Najeriya na APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci yayin da ta hana wani tsohon dan siyasa, Douglas Egharevba, mafaka a kasar saboda alakarsa da jam’iyyun.
Jaridar Peoples Gazette ta rawaito cewa alkalin kotun, Phuong Ngo, a hukuncin da ta yanke ranar 17 ga watan Yunin 2025, ta hana dan siyasar izinin shiga kasar bayan samun shi da gaza cika sharudan dokar shige da fice ta kasar.
A cewar alkalin, “Dabi’ar wasu ’yan siyasa ’yan PDP, wadanda wasu daga cikinsu ma kusoshi ne a jam’iyyar, da wadanda suka aikata laifukan siyasa ko aka yi da yawunsu, ta yi yawan da ba zai yiwu a ki alakanta shugabancin jam’iyyun da ita ba.”
Ana sa ran dai nan ba da jimawa ba gwamnatin Najeriya za ta fitar da sanarwa kan matsayinta a hukumance, kamar yadda wani babban jami’in gwamnati ya tabbatar mana, yana mai bayyana hukuncin a matsayin abin takaici.
Ita kuwa jam’iyyar PDP, ta bakin mamba a kwamitinta na zartarwa, Timothy Osadolor, ta ce kotun na da ’yancin fadin albarkacin bakinta, amma hukuncin nata ba yak an gaskiya.
“Amma babu wata hujja a cikin ra’ayin nasu da zai sa dukkan abin da suka fada a cikin hukuncin nasu ya zama gaskiya,” in ji Timothy.
Ya ce a maimakon ayyana jam’iyya gaba dayanta a matsayin kungiyar ta’addanci, kamata ya yi kotun ta fadi sunan masu alaka da ta’addancin kai tsaye, musamman a cikin jam’aiyyar APC.
Ya kuma bayyana hukuncin a matsayin na yanke kauna da salon shugabancin gwamnatin Najeriya a karkashin Shugaba Bola Tinubu, inda ya bukaci gwamnatin da kada ta dauki lamarin da wasa.
Sai dai duk kokarinmu na jin ta bakin jam’iyyar APC da gwamnatin tarayya ya ci tura ya zuwa lokacin hada wannan rahoton.
Masu magana da yawun APC na kasa, Felix Morka da Bala Ibrahim ba su amsa kira rubutaccen sakon da wakilinmu ya tura musu ba, yayin da kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, shi ma bai amsa sakon da wakilinmu ya tura masa ba.
To said ai wani jami’in gwamnati ya tabbatar da cewa gwamnatin za ta fitar da sanarwa a kan hukuncin a hukumance da zarar ta tabbatar da sahihancin hukuncin.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Rashin aiwatar da doka na bai wa masu laifi ƙwarin guiwa — Ɗan majalisar Gombe
Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Gombe, mai wakiltar Nafada ta Kudu, Adamu A. Musa, ya zargi gwamnati da ‘yan majalisun jihar da kasa aiwatar da dokokin da suke zartarwa.
Ya ce akwai dokar da aka zartar shekaru takwas da suka gabata domin yaƙi da fyaɗe da cin zarafin mata da yara, amma har yanzu ba a aiwatar da ita ba.
Sojoji sun kashe babban Kwamandan ISWAP, Amirul Fiya a Borno Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da takiA cewarsa, majalisa tana yin doka sannan ta tura wa gwamna ya sanya hannu, amma daga baya a bar ta kamar ba ta da amfani.
Ya yi gargaɗin cewa irin wannan sakaci yana ƙara wa masu aikata laifi ƙwarin guiwa kuma yana haifar da ƙaruwar manyan laifuka.
Ya ce da ana aiwatar da dokokin, da tuni an rage irin waɗannan laifuka, amma a maimakon haka, idan aka kai rahoton laifi, masu kuɗi suna ɗaukar lauyoyi su fito da su ba tare da an hukunta su ba.
Ya kawo misalin wata ɗaliba a Kano da ake zargin shugaban makarantarsu ya kashe ta, inda tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi alƙawarin aiwatar da hukuncin kisa amma bai yi hakan ba har ya sauka daga mulki.
Haka kuma ya nuna cewa babu wani gwamna a jihohin Arewa da ya taɓa aiwatar da hukuncin kisa ga masu aikata irin waɗannan manyan laifuka.
Sai dai, ya ce zai yi duk mai yiwuwa don ganin a fara aiwatar da dokokin a jihar nan gaba kaɗan.