Zaɓen cike gurbi: An kama ’yan daba 100 a Bagwai — INEC
Published: 16th, August 2025 GMT
Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), ta tabbatar da kama aƙalla ’yan daba 100 da ake zargi da tayar da zaune-tsaye a lokacin zaɓen cike gurbi da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Bagwai a Jihar Kano.
Kwamishinan INEC na Jihar Kano, Abdu Zango, ya shaida wa manema labarai a Bagwai cewa jami’an tsaro suna aikin tabbatar da zaman lafiya domin a gudanar da zaɓen cikin lafiya.
“Dukkanin mutanen da muka gani suna kawo matsala an kama su, kuma zaɓen yana tafiya lafiya.
“Na gamsu sosai da yadda komai ke tafiya. Kayan zaɓe sun isa a kan lokaci, kuma yawancin rumfunan zaɓe sun fara aiki tun ƙarfe 8:30 na safe,” in ji shi.
Zango, ya ƙara da cewa an ɗan samu jinkiri a wasu wurare saboda matsalar sufuri da kuma yunƙurin wasu ƙungiyoyi na kawo cikas.
Amma ya ce jami’an tsaro sun shiga tsakani tare da tabbatar da doka da oda.
Ya ce ko da yake ba zai iya gane mutanen da aka kama ba, rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar masa cewa ta kama aƙalla ’yan daba 100 kuma za a gurfanar da su a gaban kuliya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan daba Bagwai Zaɓen Cike Gurbi
এছাড়াও পড়ুন:
An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
Sufeto Janar na ’Yan sandan Nijeriya, Olukayode Egbetokun, ya sanar da cewa sun aiwatar da umarnin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na janye dakarunsu daga gadin ɗaiɗaikun mutane da ake kira VIP.
IG Egbetokun ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai a yau Alhamis, yana mai cewa zuwa yanzu sun janye dakaru 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya.
Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da Olympiacos An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji“Wannan karon za mu aiwatar da umarnin da kyau saboda umarnin shugaban ƙasa ne,” in ji shi.
“Babu wani gwamna, ko minista, ko abokaina da za su kira su takura min saboda sun san cewa umarnin shugaban ƙasa ne. Ina kuma da tabbacin cewa ba za su uzzura wa kwamashinonin ’yan sanda ba ma.”
Ya ƙara da cewa za su tura jami’an da aka janye zuwa “wuraren da aka fi buƙatarsu, musamman a wannan lokaci mai muhimmanci.”
Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Shugaba Bola Tinubu ya dakatar da aika ’yan sanda ga manyan mutane domin ba su tsaro na musamman, yana mai mayar da su zuwa aikin tsaro da ya shafi al’umma baki ɗaya.
Kazalila, a ranar Laraba, 26 ga watan Nuwamba ne Tinubun ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro a faɗin ƙasar, inda ya bayar da umarnin a ɗauki matakan gaggawa domin magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta.
Shugaban ya ce a ɗauki sababbin ’yan sanda 20,000, ƙari a kan guda 30,000 da ya fara amincewa a ɗauk, wanda za a yi amfani da sansanonin horar da masu yi wa ƙasa hidima wajen horar da sababbin ’yan sandan da za a ɗauka.