Zaɓen cike gurbi: An kama ’yan daba 100 a Bagwai — INEC
Published: 16th, August 2025 GMT
Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), ta tabbatar da kama aƙalla ’yan daba 100 da ake zargi da tayar da zaune-tsaye a lokacin zaɓen cike gurbi da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Bagwai a Jihar Kano.
Kwamishinan INEC na Jihar Kano, Abdu Zango, ya shaida wa manema labarai a Bagwai cewa jami’an tsaro suna aikin tabbatar da zaman lafiya domin a gudanar da zaɓen cikin lafiya.
“Dukkanin mutanen da muka gani suna kawo matsala an kama su, kuma zaɓen yana tafiya lafiya.
“Na gamsu sosai da yadda komai ke tafiya. Kayan zaɓe sun isa a kan lokaci, kuma yawancin rumfunan zaɓe sun fara aiki tun ƙarfe 8:30 na safe,” in ji shi.
Zango, ya ƙara da cewa an ɗan samu jinkiri a wasu wurare saboda matsalar sufuri da kuma yunƙurin wasu ƙungiyoyi na kawo cikas.
Amma ya ce jami’an tsaro sun shiga tsakani tare da tabbatar da doka da oda.
Ya ce ko da yake ba zai iya gane mutanen da aka kama ba, rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar masa cewa ta kama aƙalla ’yan daba 100 kuma za a gurfanar da su a gaban kuliya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan daba Bagwai Zaɓen Cike Gurbi
এছাড়াও পড়ুন:
2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe
“Muna kira ga majalisar kasa da ta yi la’akari da shirin gyaran tsarin kudurorin zabe cikin gaggawa. Amincewa da dokar cikin lokaci yana da muhimmanci ga shirinmu na gudanar da zabe a 2027.
“Rashin tabbas game da tsarin doka na zabe na iya kawo matsaloli masu yawa ga ayyukan hukumar INEC yayin da lokacin zabe ke karatowa,” in ji shi.
Shugaban INEC ya bayyana cewa hukumarsa ta aiwatar da shawarwarin da aka mika mata kai tsaye a rahoton EU na zaben 2023.
“An dauki mataki kan wasu bangarori na shawarwarin da ake bukatar hukumar ta aiwatar da su. Haka kuma, ana daukar mataki kan shawarwarin da suka shafi fannoni da dama wadanda ake bukatar hadin gwiwa tsakanin INEC da sauran hukumomi da masu ruwa da tsaki yayin da ake jiran kammala bitar sake fasalin shari’a da majalisar kasa ke yi,” in ji shi.
A nasa kalamun, Mista Barry Andrews ya yaba da muhimmancin Nijeriya a dimokuradiyyar duniya, yana bayyana aikin EU na 2023 a matsayin daya daga cikin manyan aikace-aikace ga dukkan kasashen duniya.
“Aikinmu shi ne taimakawa wajen samun ci gaban na aiwatar da shawarwarin daga zabukan shekarar 2023. Mun lura da manyan ci gaba a wasu fannoni da dama, ko da yake wasu kalubale suna nan yadda suke, musamman wadanda suka shafi shari’a da gudanarwa da tsarin gyara fasalin kundin tsarin mulki,” in ji shi.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA