Zaɓen cike gurbi: An kama ’yan daba 100 a Bagwai — INEC
Published: 16th, August 2025 GMT
Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), ta tabbatar da kama aƙalla ’yan daba 100 da ake zargi da tayar da zaune-tsaye a lokacin zaɓen cike gurbi da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Bagwai a Jihar Kano.
Kwamishinan INEC na Jihar Kano, Abdu Zango, ya shaida wa manema labarai a Bagwai cewa jami’an tsaro suna aikin tabbatar da zaman lafiya domin a gudanar da zaɓen cikin lafiya.
“Dukkanin mutanen da muka gani suna kawo matsala an kama su, kuma zaɓen yana tafiya lafiya.
“Na gamsu sosai da yadda komai ke tafiya. Kayan zaɓe sun isa a kan lokaci, kuma yawancin rumfunan zaɓe sun fara aiki tun ƙarfe 8:30 na safe,” in ji shi.
Zango, ya ƙara da cewa an ɗan samu jinkiri a wasu wurare saboda matsalar sufuri da kuma yunƙurin wasu ƙungiyoyi na kawo cikas.
Amma ya ce jami’an tsaro sun shiga tsakani tare da tabbatar da doka da oda.
Ya ce ko da yake ba zai iya gane mutanen da aka kama ba, rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar masa cewa ta kama aƙalla ’yan daba 100 kuma za a gurfanar da su a gaban kuliya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan daba Bagwai Zaɓen Cike Gurbi
এছাড়াও পড়ুন:
Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar
Sabuwar mai bada shawara kan harkokin lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya, Maryam Bukar-Hassan (Alhan_islam) ta bayyana cewa samar da dauwamammen zaman lafiya a duniya shi ne fatansu.
Maryam ta bayyana hakan ne a lokacin da babban jami’in kula da ayyukan jin ƙai na Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya, Mohammed Malick Fall, ke maraba da ita a ofishin majalisar da ke Abuja.
An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9Mohammed ya jaddada muhimmancin samar da zaman lafiya, yana mai cewa zaman lafiya wani abu ne da ake buƙata don jin daɗin rayuwar ɗan Adam, kuma idan ba a same shi ba, ci gaban dimokuraɗiyya da kuma ’yancin ɗan Adam ba zai samu ba.
Ya bayyana damuwarsa kan yadda aka sake samun ɓullar tashe-tashen hankula a Nijeriya da ma duniya baki ɗaya, yana mai cewa hakan koma baya ne ga ci gaban da aka samu tun kafuwar MDD shekara 80 da suka gabata.
Da take nata jawabin Maryam Bukar Hassan ta ce, akwai buƙatar a samar da wani shiri na kawo sauyi wajen samar da zaman lafiya mai ɗorewa.
Har ila yau, Mohammed Fall ya yaba da yadda aka naɗa Maryam Bukar-Hassan a matsayin, ya ce hakan yazo a daidai lokacin da ya dace kuma mai mahimmanci, yana mai bayyana irin ƙarfin gwiwar da yake da shi akanta na za ta sauke nauyin da aka ɗora mata, mussaman wajen isa ga al’umma da matasa ta hanyoyin diflomasiya.
Yana mai cewa, “Ku ne muryar matasa, muryar jagorancin mata,” in ji shi. Ya kuma jaddada irin rawar da taka wajen tsara makomar neman zaman lafiya.
Ya kuma bayyana cewa, nauyin da ke kanta ya yi fice a Nijeriya har zuwa ayyukan da duniya ke yi. Duk da irin rawar da take takawa a duniya, Fall ya ba ta tabbacin goyon bayan Majalisar Ɗinkin Duniya.
Hakazalika Maryam Bukar-Hassan ya jaddada cewa, idan har ba zaman lafiya ba, yadda za a iya cimma muradun ci gaba mai ɗorewa (SDGs) kuma zai kasance mara amfani.
“Ba maganar talauci idan zaman lafiya da yin adalci sun tabbata,” in ji ta,
Ta kuma ƙara da cewar, tabbatar da yunƙurin zaman lafiya ta hanyar haɗa harsunan asalin ƙabilu da al’adu na gargajiya ne fatanmu dole mu haɗa da harshen Ingilishi,” in ji ta.
Idan har muna son mu kai ga cimma nasara dole ne, mu komo hanyar yadda da al’ummominmu suka tsara. Wannan hanya na nufin tabbatar da gina zaman lafiya mai ɗorewa, musamman a yankunan da asalin al’adu ke taka muhimmiyar rawa a cikin zamantakewa.