Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura
Published: 13th, August 2025 GMT
Gwamnatin jihar Katsina ta ce shirye-shirye sun kankama domin bin sahun sauran sassan duniya a yayin bikin Ranar Hausa ta Duniya a za ake gudanarwa ranar 26 ga watan Agustan kowacce shekara.
Shugaban Hukumar Kula d Tarihi da Al’adu ta jihar, Dr Kabir Ali-Masanawa ne ya bayyana hakan yayin wani jawabi ga manema labarai a Katsina ranar Talata.
Ya ce za a yi taron ne a Fadar Sarkin Daura da ke jihar, kuma ana sa ran manyan baki daga kasashe akalla 24 za su halarta.
Masanawa ya ce wannan shi ne karo na farko da gwamnati ta shiga cikin shirya bikin, inda ya ce hatta Gwamnan jihar, Dikko Umaru Radda ya tsaya tsayin daka wajen ganin bikin ya yi nasara.
DAGA LARABA: Yadda sinadaran dandanon abinci ke yin illa ga lafiya Fursunoni 16 sun tsere daga gidan yarin KeffiShugaban ya ce ranar na fito da tarihi da al’adun Hausawa a fadin duniya, wadanda suka warwatsu a kasashen duniya daban-daban.
Ya kare da cewa, “Kwanan nan mun ziyarci Fadar Sarkin Daura inda muka jaddada masa alfaharin da muke yi da harshen Hausa.
“Ana sa ran a bana, akwai akalla kasashe 24 da za su halarci bikin na Daura,” in ji shi.
Shugaban hukumar ya kuma ce bikin zain una al’adun Hausawa ta hanyar kade-kade da raye-raye da tufafi da abincin Hausawa.
Daga nan sai ya baki masu shirin shiga jihar tabbacin cewa akwai zaman lafiya kuma suna kokari wajen bunkasa tsaro, ta yadda jihar za ta ci gaba da zama wajen yawon bude ido ga baki.
Daga cikin kasashen da ake has ashen zuwan bakin har da Burtaniya da Amurka da Saudiyya da Ghana da kuma kasar Netherlands, a karon farko.
Kiyasi dai ya nuna Hausa shi ne yare na 11 da aka fi amfani da shi a duniya inda yake da masu amfani da shi sama da miliyan 150.
An dai fara bikin ranar ne a shekara ta 2015 kuma duk shekara akan gudanar da babban taro a sassa daban-daban na duniya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Daura Ranar Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
Ana zargin wata amarya da yi wa angonta yankan rago kwana uku bayan ɗaurin aurensu a Jihar Katsina.
Angon mai suna Abubakar Abdulkarim da aka fi sani da Dan Gaske, ana zargin ya rasa ransa bayan da amaryar ta yi amfani da wuƙa wajen halaka shi.
Shaidu sun ce ta yi masa mummunan rauni a wuya wanda ya yi sanadiyyar mutuwarsa.
Angon da amaryarsa suka daura aure ne a ranar Alhamis, 18 ga Nuwamba, 2025, amma farin cikin aure ya rikide zuwa makoki a ranar Lahadi da rana lokacin da lamarin ya faru.
Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke FuskantaWani ɗan uwansa mai suna Aminu Danladi ya ce cewa sun yi taro da marigayin da safiyar ranar, suna shirya ziyarar ’yan uwansu da za a kai da yamma.
Ya ce daga baya ango ya koma gida domin shiri, sai kuma aka ji labarin an same shi kwance a cikin jini babu rai.
Aminu ya kuma ƙaryata jita-jitar da ake yaɗawa cewa auren dole ne aka yi wa ma’auratan, inda ya tabbatar da cewa dangantakarsu ta kasance lafiya kafin aure.
Majiyoyi sun ce matar, ’yar asalin Katsina, ta taɓa yin aure a baya, abin da ake zargin dangin mijin ba su sani ba.
An ce bayan faruwar lamarin amaryar ta ruɗe inda ta je gidan maƙwabta tana neman abinci. Wannan hali ya sa tsofaffin mata zargin akwai matsala, suka bi ta gida inda suka tarar da gawar mijin, suka kuma sanar da jami’an tsaro.
Rundunar ’Yan Sanda ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce ta fara gudanar da bincike a kai.
Kakakin ’yan sanda na jihar, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ya ce an kama mutum ɗaya da ake zargi da hannu a lamarin, kuma bincike na ci gaba.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Katsina, CP Bello Shehu, ya tabbatar da cewa za a gudanar da bincike mai zurfi, tare da kira ga jama’a da su bayar da bayanai masu amfani.