Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura
Published: 13th, August 2025 GMT
Gwamnatin jihar Katsina ta ce shirye-shirye sun kankama domin bin sahun sauran sassan duniya a yayin bikin Ranar Hausa ta Duniya a za ake gudanarwa ranar 26 ga watan Agustan kowacce shekara.
Shugaban Hukumar Kula d Tarihi da Al’adu ta jihar, Dr Kabir Ali-Masanawa ne ya bayyana hakan yayin wani jawabi ga manema labarai a Katsina ranar Talata.
Ya ce za a yi taron ne a Fadar Sarkin Daura da ke jihar, kuma ana sa ran manyan baki daga kasashe akalla 24 za su halarta.
Masanawa ya ce wannan shi ne karo na farko da gwamnati ta shiga cikin shirya bikin, inda ya ce hatta Gwamnan jihar, Dikko Umaru Radda ya tsaya tsayin daka wajen ganin bikin ya yi nasara.
DAGA LARABA: Yadda sinadaran dandanon abinci ke yin illa ga lafiya Fursunoni 16 sun tsere daga gidan yarin KeffiShugaban ya ce ranar na fito da tarihi da al’adun Hausawa a fadin duniya, wadanda suka warwatsu a kasashen duniya daban-daban.
Ya kare da cewa, “Kwanan nan mun ziyarci Fadar Sarkin Daura inda muka jaddada masa alfaharin da muke yi da harshen Hausa.
“Ana sa ran a bana, akwai akalla kasashe 24 da za su halarci bikin na Daura,” in ji shi.
Shugaban hukumar ya kuma ce bikin zain una al’adun Hausawa ta hanyar kade-kade da raye-raye da tufafi da abincin Hausawa.
Daga nan sai ya baki masu shirin shiga jihar tabbacin cewa akwai zaman lafiya kuma suna kokari wajen bunkasa tsaro, ta yadda jihar za ta ci gaba da zama wajen yawon bude ido ga baki.
Daga cikin kasashen da ake has ashen zuwan bakin har da Burtaniya da Amurka da Saudiyya da Ghana da kuma kasar Netherlands, a karon farko.
Kiyasi dai ya nuna Hausa shi ne yare na 11 da aka fi amfani da shi a duniya inda yake da masu amfani da shi sama da miliyan 150.
An dai fara bikin ranar ne a shekara ta 2015 kuma duk shekara akan gudanar da babban taro a sassa daban-daban na duniya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Daura Ranar Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
Wani sabon rikici ya barke a jihar Sokoto inda ‘yan bindiga sun kai hari a wani masallaci a kauyen Marnouna da ke karamar hukumar Wurno, inda suka kashe akalla mutum daya tare da yin awon gaba da wasu da ba a tantance adadinsu ba a lokacin da ake sallar isha.
Shugaban jam’iyyar APC reshen jihar Sokoto, Alhaji Isah Sadik Achida, wanda ya fito daga yankin ya tabbatar da faruwar harin inda ya jaddada cewa maharan sun kuma kashe shugaban kungiyar masu sayar da babura na yankin a yayin farmakin.
Achida ya ci gaba da cewa, kwana biyu kacal kafin harin masallacin, ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyuka biyu da ke makwabtaka da su, Gidan Taru da Kwargaba, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna garin tare da jaddada cewa ‘yan bindigar sun kuma kashe wani dan uwa tare da kama iyalansa baki daya.
A cewar shugaban jam’iyyar APC, ‘yan ta’addan na kokarin kafa sansani a yankin domin fadada ayyukansu.
Achida ya tabbatar wa mazauna jihar cewa gwamnatin jihar da jami’an tsaro suna bakin kokarinsu domin yakar matsalar.
Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Sakkwato, ASP Abubakar Rufa’i, ya tabbatar wa gidan rediyon Najeriya faruwar lamarin inda ya ce a yanzu ‘yan fashin na kai hare-hare a lokutan damina domin kai hare-haren ba tare da an gano su ba.
NASIR MALALI