Ba mu da tabbas na ci gaba da rijistar kaɗa ƙuri’a a Borno – INEC
Published: 15th, August 2025 GMT
Hukumar Zaɓe Mai zaman kanta ta Ƙasa a Jihar Borno ta bayyana cewa, babu tabbas na gudanar da aikin rijistar masu kaɗa ƙuri’a na shekarar 2025/2026 a wasu Ƙananan hukumomin Jihar huɗu don matsalar tsaro.
Ƙananan hukumonin sun haɗa da: Ƙaramar Hukumar Abadam da Guzamala da Marte da Kala-Balge
Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe An sake ceto matafiya 10 da aka sace a KogiBayanin hakan dai ya fito ne daga bakin Kwamishinan zaɓe na Jihar Borno, Abubakar Ahmad Ma’aji a jawabinsa ga manema labarai a Maiduguri, a wani ɓangare na shirye-shiryen fara gudanar da aikin rijistar masu kaɗa kuri’a a ranar Litinin da ke tafe.
Kamar yadda Kwamishinan Hukumar zaɓen ke bayyanawa, INEC ta mayar da rijistar masu kaɗa ƙuri’a na ci gaba da gudana a Ƙaramar hukumar Abadam zuwa kan hanyar Baga daura da ofishin Yerwa Peace.
Haka nan shi kuma aikin rijistar masu kaɗa ƙuri’a na Ƙaramar hukumar Guzamala an mayar da shi a sashen kashe gobara na rukunin gidaje 1,000.
Sauran Ƙananan hukumomin kamar Ƙaramar hukumar Kala-Balge an mayar da aikin ya zuwa makarantar firamare ta Goni Kachalari da ke birnin na Maiduguri.
Shi kuma aikin rijistar masu kaɗa ƙuri’a na Ƙaramar hukumar Marte an mayar da shi ya zuwa Kachamai, waɗanda dukkansu suna cikin birnin Maiduguri ne.
Don haka Kwamishinan ya yi kira ga mutanen waɗannan ƙananan hukumomin da su yi haƙuri da wannan canji da aka samu an yi ne da kyakkyawar manufar da duk wanda abin ya shafa zai samu rijistar katinsa na kaɗa ƙuri’a cikin kwanciyar hankali.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Abadam da Guzamala da Marte da Kala Balge aikin rijistar masu rijistar masu kaɗa kaɗa ƙuri a na Ƙaramar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Cutar amosanin jini wacce aka fi sani da cutar sikila na cigaba da barazana ga rayukan masu dauke da ita.
Wannan cuta na saka masu ita da ‘yan uwan su cikin halin ha’ula’i, a wasu lokutan ma tana haifar da rasa rayukan wasu dake dauke da ita.
Rahotannin Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) sun nuna cewa, kusan yara 300,000 ne ake haifa da cutar Sikila a duk shekara a fadin duniya, inda yankin Kudu da Sahara a Afirka ke dauke da kashi 75% na wannan yawan.
A Najeriya kadai, ana kiyasta cewa fiye da yara 150,000 ake haifa da cutar Sikila a kowace shekara — hakan ya sa Najeriya ke da mafi yawan masu fama da cutar Sikila a duniya.
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan cutar amosanin jini don gano yadda masu fama da ita ke ji a rayuwar su.
Domin sauke shirin, latsa nan