Alausa ya ce dakatarwar, wacce ta shafi dukkan nau’o’in manyan makarantun gwamnatin tarayya an yi hakan ne da nufin dakatar da maimaici da barnatar da dukiyar gwamnati, inda za a yi amfani da kudin domin inganta makarantun da ake da su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Gombe za ta ƙirƙiri sabbin ƙananan hukumomi 13

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya miƙa ƙudiri zuwa Majalisar Dokokin Jihar domin neman amincewarta a ƙirƙiri sabbin ƙananan hukumomi 13.

Gwamnan, ya bayyana cewa wannan mataki zai taimaka wa gwamnati wajen kusantar al’umma, da ayyukan raya ƙasa.

Jama’a sun koka kan rashin kammala aikin titi a Kafanchan Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki

Sabbin ƙananan hukumomin da ake shirin ƙirƙira za su fito daga ƙananan hukumomin da ake da a jihar.

A cewar gwamnan sabbin ƙananan hukumomin za su mayar da hankali kan samar da tsaro, ilimi, kiwon lafiya, gina muhalli da sauran muhimman ayyukan jama’a musamman a yankunan karkara.

Za su kuma yi aiki tare da masarautu da shugabannin al’umma wajen tabbatar da zaman lafiya, bunƙasa ci gaba da magance matsalolin tsaro bisa tanadin dokar masarautu ta jihar.

Sabbin ƙananan hukumomin da za a ƙirƙira su ne Akko Arewa mai hedikwata a Amada, Akko Yamma mai hedikwata a Pindiga, Balanga Kudu mai hedikwata a Bambam, Billiri Yamma mai hedikwata a Tal, Dukku Arewa mai hedikwata a Malala, Funakaye Kudu mai hedikwata a Tongo.

Akwai Gombe Kudu mai hedikwata a Bolari, Kaltungo Gabas mai hedikwata a Wange, Kwami Yamma mai hedikwata a Bojude, Nafada Kudu mai hedikwata a Birin Fulani.

Sauran sun haɗa da Pero-Chonge mai hedikwata a Filiya, Yamaltu Gabas mai hedikwata a Hinna, da Yamaltu Yamma mai hedikwata a Zambuk.

Domin tabbatar da nasarar aiwatar da wannan shiri, ƙudirin ya tanadi kafa kwamiti na wucin gadi da zai jagoranci kowace ƙaramar hukuma har zuwa lokacin da za a gudanar da zaɓe.

Za a aiwatar da shirin a matakai tare da tsare-tsaren aiki, tsarin ma’aikata da kasafin kuɗi da zai tabbatar da harkokin gudanarwa.

Gwamnan, ya roƙi majalisar dokokin jihar da ta duba ƙudirin cikin gaggawa tare da amincewa da shi.

Sannan ya kira ga al’ummar jihar da su goyi bayan shirin wanda ya ce zai bunƙasa mulki da ci gaban Jihar Gombe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Zartaswa ta dakatar da ƙirƙirar sabbin manyan makarantu a Nijeriya
  • Gwamnatin Gombe za ta ƙirƙiri sabbin ƙananan hukumomi 13
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukumar Rano Na Tsawon Watanni Uku
  • Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba
  • ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
  • PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
  • Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
  • Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan