Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya karbi bakuncin Mataimakin Ministan Noma na Jamhuriyar Liberia, David Akoi, a wata ziyara ta musamman domin nazarin dabarun noman shinkafa a jihar, wadda ita ce kan gaba a fitar da shinkafa a Najeriya.

A yayin ziyarar ban girma a fadar gwamnati da ke Dutse, Mista Akoi ya ce wannan ziyara za ta ba tawagarsa damar fahimtar dabarun noma da sarrafa shinkafa, samun horo a aikace, tare da koyo game da dukkan sassan harkar noman shinkafa.

Ya bayyana cewa, wannan zai taimaka wa Liberia rage dogaro da shinkafar da ake shigowa da ita daga waje.

“A Liberia muna cin shinkafa safe, rana da dare. A shekarar 1979, an yi tarzomar shinkafa da ta kifar da gwamnatin Shugaba William R. Tolbert bayan yunkurin kara farashin shinkafa,” in ji shi. “Yanzu haka muna shigowa da kimanin kashi 70 cikin dari na shinkafar da muke ci.”

Ya ce gwamnatin Liberia ta kuduri aniyar samar da aƙalla kashi 70 cikin dari na bukatar shinkafar cikin gida. Ya bayyana cewa Shugaba Joseph Boakai ya zabi Najeriya, musamman Jihar Jigawa, saboda irin ci gaban da ta samu a harkar noman shinkafa.

“Mun zo ne domin koyo daga Jigawa yadda ta samu wannan nasara, da dabarun da ta yi amfani da su wajen shawo kan matsalolin noma.” In ji shi. “Manufarmu ita ce mu aiwatar da irin wannan nasara a kasarmu.”

Da yake mayar da martani, Gwamna Namadi ya yaba wa Liberia bisa zaben Jigawa, yana mai cewa wannan hadin gwiwa zai bai wa bangarorin biyu damar musayar dabaru da gogewa da za su amfani bangarorin noman su. Ya jaddada cewa noma ita ce ginshikin tattalin arzikin Jigawa.

“A shekarar 2023, Jigawa na noman kadada 60,000 zuwa 70,000 na shinkafa. Amma a 2024, mun kai sama da kadada 200,000, kuma bana muna fatan kaiwa kadada 300,000. Burinmu shi ne mu samar da kashi 50 cikin dari na shinkafar da Najeriya ke bukata nan da 2030,” in ji shi.

Gwamnan ya bayyana cewa jihar na mai da hankali kan noman rani domin rage illar sauyin yanayi. “Muna gyara madatsun ruwa 10 da ke jihar, wanda hakan ke kara fiye da kadada 4,500 ga filayen noma,” In ji shi.

Don kara yawan amfanin gona, gwamnatin jihar ta samar da sababbin taraktoci 300 da  kayayyakin aikin su, injinan girbi 60, injinan shuka 150, da sauran kayan noma na zamani. Kowacce cikin mazabu 30 a jihar tana da akalla taraktoci 10 da ake ba manoma kananan haya a farashi rahusa rahusa.

Gwamna Namadi ya tabbatar da cewa Jigawa za ta ci gaba da zuba jari a harkokin noma na zamani don karfafa sashen shinkafa, tare da bai wa Liberia goyon baya a yunkurinta na cimma wadatar shinkafa a cikin gida.

 

Usman Muhammad Zaria 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi

Gwamnonin jihohin kudu maso yammacin Najeriya sun bada sanarwan cewa lokacin kafa yansandan jihohi ya yi, har’ila yau dakuma karfafa kula da dazuzzukan kasar saboda magance matsalolin tsaro da suka addabi kasar.

Jaridar Daily Trust ta nakalto gwamnonin na fadar haka a jiya Litinin bayan taron gwamnonin shiyar kudu maso yammacin kasar da suka gudanar a birnin Ibadan na jihar Oyo. Gwamnonin 6 sun yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya aika masu gadin dazuzzuka a shiyar kudu maso yammacin kasar don tabbatar da tsaronsu , sannan gwamnonin jihohin guda  shida ne zasu dauki nauyin kula da jami’an tsaron.  Labarin ya kara da cewa shugaban gwamnonin kuma gwamnan jihar Lagos Babajide Sanwo-Olu ne ya karanta jawabin bayan taron gwamononin 6.  Sauran gwamnonin sun hada da Dapo Abiodun na jihar Ogun, Biodun Oyebanji na jihar  Ekiti, Lucky Aiyedatiwa na jihar Ondo, Ademola Adeleke na jihar Osun, wanda mataimakinsa , Yerima  Kola Adewusi ya wakilta sai kuma gwamna mai masaukin baki Seyi Makinde na jihar Oyo.  Taron gwamnonin ya yabawa gwamnatin tarayyar kan kokarin da take yi na magance matsalolin tsaro a arewacin kasar, suna kuma gabatar da alhininsu gareta saboda abubuwan bakin ciki da suka faru a jihohin Kebbi, Naija da kuma Kwara.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Dubban Alummar Kasar Tunisia Ne Suka Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Mulkin Kama Karya A Kasar November 24, 2025 Mutane 6 Ne Suka Mutu Sakamakon Harin Kunar Bakin Wake Da Aka Kai A Peshavar Na Kasar Pakistan November 24, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare   November 24, 2025 Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta November 24, 2025 Wakilin MDD Ya Bukaci Goyon Bayan Iran Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yamen November 24, 2025 Yara 50 Da Aka Sace A Najeriya Sun Tsere Daga Hannun Barayin Daji November 24, 2025 Habasha: Bayan Shekaru 10,000 Dutsen Hayli Gubbi Ya Yi Aman Wuta November 24, 2025 Iran Ta Mika Ta’aziyyarta Ta Shahadar Kwamandan Mayakan Hizbullah November 24, 2025  Hizbullah Ta Sanar Da Shahadar Kwamandan Jihadi Haisam al-Tabtabai November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja
  • Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi