Aminiya:
2025-08-13@13:36:47 GMT

‘Zan iya shiga mummunan yanayi idan Dangote bai aure ni ba’

Published: 13th, August 2025 GMT

Wata ’yar siyasa a jihar Bauchi mai suna Aishatu Haruna, ta ce ta shafe shekaru shida tana dakon soyayyar attajirin nan na Afirka, Alhaji Aliko Dangote a ranta, inda ta ce za ta iya shiga mummunan hali idan bai aure ta ba.

Ta ce sau uku tana yin mafarkin ta aure shi, kuma ba ta jin za ta iya auren wani ba shi ba a duniya.

A cikin wata tattaunawarta da gidan rediyon Albarka da ke jihar Bauchi, Aishatu, wacce aka fi sani da Gimbiyar Mawakan Bauchi, ta kuma ce sau uku tana zuwa kamfanin attajijin na Obajana, ko za ta hadu da shi a can.

Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura Lafiyar Tinubu kalau – Soludo

Aishatu wacce a 2019 ta yi takarar neman zama Majalisar Jiha dai ta wallafa hotonta ne dauke da katin gayyatar daurin aurenta da attajirin a shafukan sada zumunta, inda ta ce tana ganin ta wannan hanyar ce sakonta zai isa gare shi.

A cewarta, “Ita soyayya a zuci take, kuma ni na gamsu shi nake so, saboda yadda yake amfani da dukiyar da Allah ya ba shi wajen hidimta wa al’umma ba iya Najeriya ba, har ma da Afirka.

“Kusan shekara shida ke nan da farawar abin. Akwai lokacin ma da na yi tattaki na tafi har kamfaninsa na siminta da ke Obajana a jihar Kogi da nufin na gan shi har sau uku, amma bai yiwu ba.

“Dalilin da ya sa na buga katin shi ne saboda na san nan ce hanya mafi sauri da zai san da ni, kuma na san babu abin da ya gagari Allah,” in ji ta.

Sai dai ta tsaya kai da fata cewa ba don dukiyarsa take son shi ba, kawai ji ta yi shi kadai ne ya kwanta mata a ransa.

“Babu wanda aka haifa da dukiya, kuma ba don ita nake son shi ba, don haka ba maganar kwarya ta bi karya don baa bin da ya gagari Allah. Ni kawai yana burge ni ne,” in ji ta.

Ta ce ta gaji da dakon soyayyar a zuciyarta, shi ya sa yanzu ta fito da ita a shafukan sada zumuntar domin kada ta shiga wani halin.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Yi Gargadi Game Da Sabawa Dokokin Fitillun Bada Hannu A Titinan Jihar

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayar da gargadi game da hawan keken masu kananan shekaru da rashin biyayya ga fitilun ababen hawa a cikin babban birnin Kano.

 

 

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanya wa hannu, kuma aka rabawa manema labarai a Kano.

 

Gargadin na zuwa ne bayan an samu munanan hadurran kan tituna guda 16 a cikin watan Agustan 2025, wanda ya yi sanadin jikkata da asarar dukiyoyi.

 

 

Rundunar ta lura cewa hawan keken ƙananan yara yana haifar da babban haɗari ga mahaya da sauran masu amfani da hanyar.

 

 

An shawarci iyaye da masu kula da su da su guji barin ‘ya’yansu da ba su da shekaru su yi amfani da keken mai kafa uku, domin hakan zai jawo hukunci mai tsanani a karkashin dokar.

 

 

Rundunar ta kuma lura da yanayin rashin biyayya ga fitilun ababen hawa da kuma dokokin hanya daga wasu masu amfani da hanyar.

 

 

“Wannan dabi’a tana haifar da cunkoson ababen hawa da ba dole ba, da kuma hadurran da za a iya kaucewa, da jefa rayukan mutane cikin hadari da kuma kawo cikas ga zirga-zirgar ababen hawa.”

 

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kebe jami’an tsaro domin tabbatar da bin ka’idojin zirga-zirga.

 

Rundunar ta bukaci duk ‘yan kasar da su bi dokokin hanya da kuma bayar da rahoton duk wani abu na hawan keken kanana, tukin ganganci, ko wasu keta haddi.

 

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaro na rayuka da dukiyoyi a jihar.

 

Abdullahi jalaluddeen/Kano

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita
  • ‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi
  • EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi
  • An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
  • Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Yi Gargadi Game Da Sabawa Dokokin Fitillun Bada Hannu A Titinan Jihar
  • Tehran: Kasar Lebanon Tana Da yencin Kare Kanta Da Makamanta
  • An Yi Allah Wadai Da Hana Amfani Da Hijabi A Jami’ar LandMark, Omu-Aran Kwara
  • Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya