Motar tifa ta murƙushe ɗalibai biyu har lahira a Bayelsa
Published: 14th, August 2025 GMT
Wasu mutum biyu da ake zargin ɗaliban jami’a ne a Jihar Bayelsa sun mutu bayan wata mota ƙirar tifa ta murƙushe su lokacin da suke kan babur mai ƙafa uku a kan hanyar Tombia zuwa Ammassoma.
Daily Trust ta samu rahoton cewa haɗarin wanda ya afku a ranar Talata, ya kuma sa wasu fasinjojin da ke cikin babur ɗin sun samu munanan raunuka.
A cewar wasu mazauna yankin, haɗarin ya afku ne a kusa da wani lanƙwasa mai haɗarin gaske a kan babbar hanyar, sakamakon rashin kyan hanyar da kuma gudun wuce ƙima.
Sun ce babbar motar tifa na gangarowa kan tudu cikin sauri lokacin da ta ƙwacewa direban ta kuma afka kan babur ɗin.
Wani ɗan kasuwa mai suna Godspower Okolo, ya shaida wa manema labarai cewa direban tifa ɗin yana tafiya da sauri, kuma a lokacin da ya yi yunƙurin karkatar da motar abin ya citura.
Ya ce, “Keke (Babur mai ƙafa uku) ba ta da damar kaucewa hatsarin, domin kuwa tifa ɗin ta riga ta yi kusa da shi, mun yi ta ƙorafin yadda direbobin manyan motocin dakon kaya suke yi a wannan hanyar tsawon shekaru, amma babu abin da ya canza.
“Haɗarin ya sa babur ɗin ya lalace ba tare da an gane fasinjojin cikin ba, wasu masu jinƙai ne suka garzaya wurin da lamarin ya faru, inda suka kwashe waɗanda suka tsira daga haɗarin tare da kai waɗanda suka jikkata zuwa cibiyar lafiya ta tarayya da ke Yenagoa, daga baya aka kwashe gawarwakin waɗanda suka mutu zuwa ɗakin ajiye gawa na kusa.
“Wannan lamarin ya sake sabunta kiraye-kirayen a tsaurara matakan tsaro, ya kamata hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) da rundunar ’yan sanda ta jihar su ƙara yin sintiri, da ɓullo da na’urorin hana gudu, da kuma gudanar da binciken ababan hawa kan manyan motoci,” in ji shi.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Bayelsa, DSP Musa Muhammad, ya tabbatar da faruwar haɗarin, inda ya ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano musabbabin haɗarin motar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bayelsa Hatsarin tifa
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Zartaswa ta dakatar da ƙirƙirar sabbin manyan makarantu a Nijeriya
Gwamnatin Tarayya ta yanke shawarar dakatar da ƙirƙirar sabbin manyan makarantu har na tsawon shekaru bakwai masu zuwa a duk faɗin Nijeriya.
Dakatarwar ta shafi ƙirƙirar sabbin jami’o’i, kwalejojin ilimi da kuma kwalejojin kimiyya da fasaha na tarayya kamar yadda Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) ta tabbatar.
Tinubu zai tafi ziyarar ƙasashe 3 An naɗa sabon Sarkin Alkaleri a BauchiWannan mataki, a cewar Ministan Ilimi Dakta Olatunji Alausa, an ɗauke shi ne domin rage yawan makarantun da ba a amfani da su yadda ya kamata, lamarin da zai ba da damar mayar da hankali wajen gyara da inganta waɗanda ake da su yanzu.
Da yake zantawa da manema labarai bayan taron na FEC a fadar shugaban ƙasa ranar Laraba, Alausa ya bayyana cewa binciken da aka gudanar ya nuna cewa samun damar shiga jami’a a Nijeriya “ba ita ce matsala ba” a halin yanzu.
Sai dai ministan ya ce yawan kafa makarantu marasa inganci da maimaita su ne ke jawo matsaloli irin su gine-ginen da ba su dace ba, ƙarancin ma’aikata, da raguwar ɗalibai.
Ya ce “akwai wasu jami’o’in gwamnatin tarayya da ke aiki ƙasa da yadda ya dace da su, inda wasu ke da ɗalibai da ba su haura 2,000 ba. A wata jami’a ma, ma’aikata 1,200 ne ke kula da ɗalibai ƙasa da 800.
“Wannan asarar kuɗin gwamnati ne, saboda a yanzu muna da jami’o’i 199, amma ƙasa da ɗalibai 100 ne suka nemi shiga kowace ta hanyar JAMB. Har ma akwai jami’o’i 34 da babu wanda ya nema gaba ɗaya,” in ji shi.