Motar tifa ta murƙushe ɗalibai biyu har lahira a Bayelsa
Published: 14th, August 2025 GMT
Wasu mutum biyu da ake zargin ɗaliban jami’a ne a Jihar Bayelsa sun mutu bayan wata mota ƙirar tifa ta murƙushe su lokacin da suke kan babur mai ƙafa uku a kan hanyar Tombia zuwa Ammassoma.
Daily Trust ta samu rahoton cewa haɗarin wanda ya afku a ranar Talata, ya kuma sa wasu fasinjojin da ke cikin babur ɗin sun samu munanan raunuka.
A cewar wasu mazauna yankin, haɗarin ya afku ne a kusa da wani lanƙwasa mai haɗarin gaske a kan babbar hanyar, sakamakon rashin kyan hanyar da kuma gudun wuce ƙima.
Sun ce babbar motar tifa na gangarowa kan tudu cikin sauri lokacin da ta ƙwacewa direban ta kuma afka kan babur ɗin.
Wani ɗan kasuwa mai suna Godspower Okolo, ya shaida wa manema labarai cewa direban tifa ɗin yana tafiya da sauri, kuma a lokacin da ya yi yunƙurin karkatar da motar abin ya citura.
Ya ce, “Keke (Babur mai ƙafa uku) ba ta da damar kaucewa hatsarin, domin kuwa tifa ɗin ta riga ta yi kusa da shi, mun yi ta ƙorafin yadda direbobin manyan motocin dakon kaya suke yi a wannan hanyar tsawon shekaru, amma babu abin da ya canza.
“Haɗarin ya sa babur ɗin ya lalace ba tare da an gane fasinjojin cikin ba, wasu masu jinƙai ne suka garzaya wurin da lamarin ya faru, inda suka kwashe waɗanda suka tsira daga haɗarin tare da kai waɗanda suka jikkata zuwa cibiyar lafiya ta tarayya da ke Yenagoa, daga baya aka kwashe gawarwakin waɗanda suka mutu zuwa ɗakin ajiye gawa na kusa.
“Wannan lamarin ya sake sabunta kiraye-kirayen a tsaurara matakan tsaro, ya kamata hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) da rundunar ’yan sanda ta jihar su ƙara yin sintiri, da ɓullo da na’urorin hana gudu, da kuma gudanar da binciken ababan hawa kan manyan motoci,” in ji shi.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Bayelsa, DSP Musa Muhammad, ya tabbatar da faruwar haɗarin, inda ya ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano musabbabin haɗarin motar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bayelsa Hatsarin tifa
এছাড়াও পড়ুন:
Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya maƙale a Guinea-Bissau bayan da sojoji suka yi juyin mulki tare da karɓe ragamar mulkin ƙasar.
Jonathan da sauran baƙi baƙi masu sanya ido kan zaɓen da aka gudanar, ba za su iya barin ƙasar ba domin sojoji sun rufe iyakokin ƙasar baki ɗaya, tare da dakatar da zaɓen gaba ɗaya.
Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniyaLamarin ya samo asali ne bayan manyan ’yan takara biyu sun yi iƙirarin samun nasara a zaɓen shugaban ƙasa da ya gudana.
Ba jimawa wasu dakarun sojin ƙasar suka hamɓarar da gwamnatin farar hula ta ƙasar.
Sun kuma sanar da dokar hana fita da kuma kama manyan jami’an da ke da alaƙa da zaɓen.
“An hamɓarar da gwamnatina,” in ji Shugaba Umaro Sissoco Embalo cikin wata tattaunawa ta waya da gidan talabijin na ƙasashen waje.
Jonathan ya je Guinea-Bissau ne a matsayin shugaban tawagar West African Elders Forum (WAEF) domin sanya ido kan zaɓen.
Ya ziyarci wasu rumfunan zaɓe a ƙasar kuma ya wallafa bayanai a kafafen sada zumunta kafin juyin mulkin.
Mutanen da ke tare da shi sun ce yana cikin ƙoshin lafiya, amma ba shi da damar barin ƙasar.
Sojojin suna kuma ƙoƙarin katse Intanet, lamarin da ya sa ake samun tangarɗa wajen sadarwa a ƙasar.
Hakan ya sa ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa suka fara nuna damuwa kan tsaron manyan ’yan siyasa da jami’an zaɓe.
A cikin wata sanarwa, Jonathan da wasu shugabannin Afirka sun yi Allah-wadai da juyin mulkin.
“Mun yi Allah-wadai da wannan yunƙuri na daƙile tsarin dimokuraɗiyya, kuma muna kira ga Tarayyar Afirka da ECOWAS su ɗauki matakin dawo da tsarin mulki,” in ji su.
Sun buƙaci mutanen Guinea-Bissau su kwantar da hankalinsu, tare da kira ga sojoji su saki dukkanin jami’an da suka kama domin a ci gaba da gudanar da zaɓe cikin lumana.