Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ
Published: 14th, August 2025 GMT
Hedikwatar Tsaro ta Ƙasa (DHQ), ta ce rahotannin da ake yaɗawa cewar ƙasurgumin ɗan bindiga Bello Turji, ya miƙa wuya ba gaskiya ba ne.
Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Tsaro, Manjo Janar Markus Kangye ne, ya sanar da hakan ga manema labarai a Abuja a ranar Alhamis yayin bayani kan ayyukan sojoji.
Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse Ba a ba mu dala 100,000 da gwamnati ta mana alƙawari ba — Super FalconsYa ce: “Turji bai miƙa wuya ba.
Turji na daga cikin manyan ’yan bindigar da ake nema ruwa a jallo a Najeriya.
Turji ya jagoranci kai wa al’umma hare-hare a Jihohin Zamfara da Sakkwato, inda suka kashe mutane da dama tare da yin garkuwa da wasu.
A kwanakin baya, an samu rahotanni cewa Turji, ya ajiye makamai kuma ya saki mut 32 da ya sace, bayan zaman sulhu da malaman addinin Musulunci suka jagoranta a Jihar Zamfara.
Amma sojojin sun bayyana cewa wannan rahotanni ba gaskiya ba ne.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Miƙa Wuya rahotanni Rundunar Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila
Nijeriya da ƙasar Isra’ila sun sake jaddada aniyarsu ta ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro a fannoni masu muhimmanci kamar yaƙi da ta’addanci, musayar bayanan sirri, samar da kuɗin tsaro da kuma horaswa ta musamman.
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwar haɗin gwiwa wadda Ƙaramar Ministar Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu, da Mataimakiyar Ministan Harkokin Waje ta Isra’ila, Sharren Haskel-Harpaz suka fitar bayan wani taro na musamman da suka gudanar ranar Litinin a Abuja.
Tinubu na amfani da EFCC ya muzguna wa ’yan adawa — Atiku Amurka da China sun dakatar da harajin da suka ƙaƙaba wa junaSanarwar, wadda mai magana da yawun Ofishin Ƙaramar Ministar Harkokin Wajen, Dokta Magnus Eze ya fitar, ta ce taron ya nuna alaƙa mai ɗorewa da muhimmanci tsakanin ƙasashen biyu.
A yayin taron, wakilan ƙasashen biyu sun tattauna batutuwan da suka shafi tsaro a duniya, musamman yaƙi da ta’addanci, da kuma inganta hulɗar siyasa da tattalin arziki.
Ministocin biyu sun yi ƙara jan hankali kan barazanar ta’addanci a duniya, inda suka ce dole ne ƙasashe su haɗa kai wajen yaƙi da shi, musamman wajen samun bayanai kan hanyoyin samar da kuɗaɗen da ke ɗaukar nauyin ta’addanci.
Haka kuma, ƙasashen biyu sun amince su ƙara haɗin kai a fannonin da suka shafi ƙasa da ƙasa tare da mara wa juna baya a muhimman batutuwa masu kawo ci gaba.
Baya ga tsaro, taron ya mayar da hankali kan amfani da fasaha da ƙirkire-ƙirkire wajen kula da iyakoki, inganta ƙwarewar makamar aiki, musayar al’adu, yawon buɗe ido, noma, da ayyukan jakadanci da shige-da-fice.
Kazalika, ƙasashen sun amince da shirye-shiryen musayar ma’aikata da ziyarar ƙara ilimi, tare da kafa tsari na musamman domin ci gaba da tattaunawa da haɗin gwiwa a nan gaba.
A wani ɓangare na taron, an yi muhawara kan fasahar zamani wadda Ambasada Janet Olisa daga Ma’aikatar Harkokin Waje ta Nijeriya ta jagoranta tare da Ambasada Sharon Bar-Li daga Ma’aikatar Harkokin Waje ta Isra’ila.