Lauyan Maïga, Cheick Oumar Konaré, ya bayyana cewa kamun bai dace ba saboda Maïga ba shi da niyyar guduwa ko lalata shaidu, yana kuma zargin cewa wannan wani mataki ne na siyasa saboda tsohon Firaministan ya daɗe yana sukar gwamnatin soja tun bayan tsawaita mulkinsu ba tare da gudanar da zaɓe ba.

Maïga, ya hau kujerar Firaminista a watan Yulin 2021 bayan gwamnatin sojoji ta yi juyin mulki, inda ya goyi bayan dakatar da shirye-shiryen zaɓe don bai wa gwamnatin soja ƙarin lokaci.

Sai dai daga baya ya fara sukar wasu matakan gwamnati, musamman bayan an dakatar da shi daga kujerarsa a watan Nuwamban 2024.

Tun bayan juyin mulkin 2020 da na 2021, Mali ta kasance ƙarƙashin mulkin soja, kuma ana zargin gwamnati da take haƙƙin ɗan adam da murƙushe ‘yan adawa.

A kwanakin baya ma an kama wasu sojoji bisa zargin kitsa juyin mulki.

Kamun Maïga ya janyo ce-ce-ku-ce a ƙasar, inda wasu ke ganin matakin a matsayin wani yunƙuri na yaƙi da cin hanci, yayin da wasu kuma ke kallonsa a matsayin dabarar murjushe ‘yan adawa, musamman a wannan lokaci da ake buƙatar haɗin kai don dawo da tsarin dimokuraɗiyya a Mali.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Tsohon Firaminista Zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ƙasa (EFCC) ta yi wa tsohon gwamnan Jihar Sokoto, Sanata Aminu Tambuwal, tambayoyi kan zargin fitar da wasu kuɗi har Naira biliyan ₦189 ta hanyar cire kuɗin daga banki.

Rahotanni sun nuna cewa, Tambuwal ya isa shalƙwatar EFCC a Abuja da misalin karfe 11:30 na safiyar yau Litinin, inda yake ci gaba da fuskantar tambayoyi daga jami’an bincike kan zargin. Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a tabbatar ko za a tsare shi ba na dogon lokaci ba.

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

Majiyoyi daga EFCC sun tabbatar da cewa an tsare shi ne kan zargin fitar da kuɗi a bainar jama’a wanda ke saɓawa dokar hana safarar kudi masu nauyi ta shekarar 2022. An ce, “Mun ware dukkan zarge-zargen da suka shafi Tambuwal, saura ya bayar da bayani.”

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya ƙi yin bayani kan lamarin lokacin da aka tuntuɓe shi. Ana sa ran tsohon gwamnan zai bayar da amsa kan yadda aka samu irin waɗannan manyan fitar kuɗi a lokacin mulkinsa a Jihar Sokoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati
  • Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • Dasuki: Kotu ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin kammala shari’ar kuɗin makamai
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara
  • EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Sakkwato Tambuwal kan zargin N189bn
  • Tinubu Ya Jinjinawa NAFDAC Bisa Matsayin Da Ta Taka A Hukumar Lafiya Ta Duniya
  • Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi
  • A Mali An Kama Sojoji Fiye da 40 Saboda Zargi da Kokarin Juyin Mulki