Aminiya:
2025-08-13@20:55:41 GMT

Sojoji sun kashe babban Kwamandan ISWAP, Amirul Fiya a Borno

Published: 13th, August 2025 GMT

Dakarun Sojin Bataliya ta 3 da ke sansanin FOB Rann, a Ƙaramar Hukumar Kala-Balge a Jihar Borno, sun daƙile wani hari da ISWAP suka kai.

Bayan tafka artabu, sojojin sun gano gawar ’yan ta’adda uku, ciki har da babban kwamandansu, Amirul Fiya.

Gwamnatin Gombe za ta ƙirƙiri sabbin ƙananan hukumomi 13 Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki

Sojojin sun bayyana cewa wannan nasara ta zama naƙaso ga shugabancin ISWAP a yankin.

Rundunar, ta ƙara jadadda ƙudirinta na kawo ƙarshen ta’addanci a Arewa maso Gabas.

Sojoji da sauran haɗin gwiwar jami’an tsaro na ci gaba da fatattakar ’yan ta’adda a yankin Arewa Maso Gabas.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Amirul Fiya Artabu hari kwamanda

এছাড়াও পড়ুন:

Za a samu ambaliya da ruwa mai karfi a jihohi 15 a Arewa —NEMA

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen ruwan sama mai karfi da zai iya haifar da ambaliya a jihohi 15 na Arewacin Najeriya da wasu wurare 68, a cikin kwanaki biyar masu zuwa.

Wannan gargadi ya fito ne daga Cibiyar Lura da Gargadin Ambaliya ta Kasa, karkashin Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya, inda aka bukaci hukumomi da al’umma su dauki matakan gaggawa don kare rayuka da dukiyoyi.

Cibiyar ta bayyana jerin jihohi da wuraren da ambaliyar za ta iya shafa sun hada da:

Adamawa: Jimeta, Mubi, Mayo-Belwa, Wuro-Bokki, Yola, Farkumo Bauchi: Jama’a Nasarawa: Keffi Kaduna: Jaji, Kafanchan, Zaria, Birnin-Gwari Katsina: Katsina, Bindawa, Kaita Kebbi: Kamba, Kangiwa, Kalgo, Ribah, Sakaba, Saminaka, Gwandu, Jega, Bunza, Birnin Kebbi, Bagudo, Argungu Kano: Bebeji, Gwarzo, Karaye, Sumaila, Tundun-wada Niger: Rijau, Ibi, Chanchaga, Magama, Mashegu, Minna, Mokwa, New-Bussa, Sarkin Pawa, Wushishi Taraba: Duchi Jigawa: Miga, Ringim, Hadejia, Dutse Yobe: Potiskum, Dapchi, Gasma, Gashua, Jakusko Zamfara: Kaura Namoda, Maradun, Shinkafi, Bungudu, Gusau Sokoto: Sokoto, Gagawa, Gada, Goronyo, Isa, Wamakko, Silame, Makira Borno: Bama Kwara: Jebba

Hukumar Kula da Halin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayyana cewa kawo yanzu mutane 140,228 a jihohi 21 ne ambaliya ta riga ta shafa a shekarar 2025.

NAJERIYA A YAU: Yadda Damina Ke Shafar Masu Ƙananan Sana’o’i Ambaliya: Mutum 165 sun mutu a Nijeriya a bana — NEMA

Hukumar Kula da Halin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayyana cewa kawo yanzu mutane 140,228 a jihohi 21 ne ambaliya ta riga ta shafa a shekarar 2025.

Alkaluman da NEMA ta fitar sun nuna ceaw ambaliyar ta riga ta raba mutane 49,205 da muhallansu, ta lalata gidaje 10,663, da kuma gonaki 9,454 a al’ummomi daban-daban.

Jihohin da ibtila’in ya fi shafa sun hada da:

Imo (28,030), Ribas (22,345), Adamwa (12,613), Abia (11,907), Delta 8,810, Borno (8,164), Kaduna (7,334), Bayelsa (5,868) da Legas (5,793).
Sauran jihohin sun hada da Akwa Ibom (5,409), Niger (3,786), Ondo (3,735), Edo (3,234), Kogi (2,825), Sokoto (1,916), Kwara (2,663), Kano (1,446), Jigawa (1,428), Gombe (972), Anambra (925), da Babban Birnin Tarayya (1,025).

Mutanen sun kunshi maza 28,505 da mata 43,531, yara 62,393, tsofaffi 5,799 da nakassu 1,887.

Da haka hukumar ta bukaci jama’a da hukumomi da su dauki matakan gaggawa don rage illar ambaliya da kare lafiyar jama’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kullum a Kamaru muke kwana, mu yini a Najeriya – Mazauna ƙauyen Borno
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
  • Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara
  • An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK
  • ‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno
  • An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
  • Za a samu ambaliya da ruwa mai karfi a jihohi 15 a Arewa —NEMA
  • Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK