’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai
Published: 14th, August 2025 GMT
Akalla ’yan ci-rani 26 sun mutu bayan jiragen ruwan da suke ciki guda biyu sun nitse a teku a kusa da tsibirin Lampedusa na ƙasar Italiya.
Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce ana hasashen ƙarin wasu mutanen kuma sun ɓace yayin da ake ci gaba da aikin ceto su.
Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin NajeriyaGalibi dai ’yan ci-ranin da suka fito daga ƙasashen Afirka na ƙoƙarin tsallakawa nahiyar Turai ne domin samun ingantacciyar rayuwa.
Ko a ranar Laraba dai ma’aikatan ceto sun ce sun ceto mutum 60 da ransu, wadanda suka hada da maza 56 da kuma mata hudu, sannan aka kai su tsibirin na Lampedusa, kungiyar bayar da agaji ta Red Cross a kasar ta Italiya ta tabbatar.
Kakakin Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (IOM), Flavio Di Giacomo, ya ce akwai mutum 95 a cikin jiragen guda biyu da suka nitse.
Ya wallafa a shafukan sada zumunta cewa, “kasancewar an ceto mutum 60 da rai, ana fargabar akwai mutum 35 da suka mutu ko kuma suka ɓace.“
Hatsarin wanda ya ritsa da ’yan ci-ranin da suka taso daga ƙasar Libya shi ne na baya-bayan nan ga mutanen da ke kokarin tsallaka teku domin shiga nahiyar Turai.
Alkaluma sun nuna daga farkon shekarar nan zuwa yanzu, akalla mutum 675 ne suka rasa ransu ta irin wannan hanyar a kan iyakokin kasashen biyu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ci rani Hatsarin Jirgin Ruwa Italiya
এছাড়াও পড়ুন:
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
Rikicin filin gona ya yi sanadin mutuwar mutum biyu tare da jikkata wasu biyu a ƙaramar hukumar Gulani da ke Jihar Yobe. Lamarin ya faru ne a daren Asabar bayan ce-ce-ku-ce tsakanin mazauna ƙauyukan Zango da Azere, waɗanda ke tsakanin iyakokin Gujba da Gulani.
Kakakin rundunar ƴansandan jihar, SP Dungus Abdulkarim, ya bayyana cewa shalƙwatar ƴansanda ta Bara ta samu kiran gaggawa daga shugaban ƙauyen Zango a ranar 9 ga Agusta, 2025, da misalin ƙarfe 11:30 na dare, inda ya sanar da cewa wasu ƴan daba daga ƙauyen Azere sun kai mummunan farmaki kan manoma.
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah Afam Osigwe Ya Zama Sabon Shugaban Kungiyar Lauyoyi Ta KasaWanda aka kashe sun haɗa da Sani Makeri, mai shekara 40, da Abdullahi Maicitta, mai shekara 35, dukkansu ƴan asalin Zango. An garzaya da waɗanda suka jikkata an kai su zuwa babban asibitin Damaturu domin samun kulawa.
SP Dungus ya ce rikicin ya samo asali ne tun bara lokacin damina, duk da ƙoƙarin hukumar ƴansanda wajen sulhu ta hanyar kwamitin daidaita iyakoki na Jiha. Kwamishinan ƴansandan jihar, CP Emmanuel Ado, ya la’anci harin tare da bayar da tabbacin cafke masu laifi, kana ya ja hankalin manoma su guji ɗaukar doka a hannu su kuma nemi sulhu ta hanyar hukumomi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp