Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukumar Rano Na Tsawon Watanni Uku
Published: 13th, August 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Rano, Alhaji Muhammad Naziru Ya’u, na tsawon watanni uku sakamakon zarge-zargen aikata ba daidai ba.
An yanke wannan hukunci ne a zauren majalisa ƙarƙashin jagorancin Shugaban Majalisar, Alhaji Jibril Isma’il Falgore, bayan kwamitin majalisar kan ƙorafe-ƙorafe ya gabatar da rahoton bincikensa.
Yayin gabatar da rahoton, Shugaban Kwamitin wanda shi ne shugaban masu rinjaye, Alhaji Lawan Hussaini Dala, ya ce binciken ya samo asali ne daga ƙorafin da kansiloli tara daga cikin goma na Rano suka sanya wa hannu.
A cewarsa, ƙorafin ya zargi shugaban da yin sakacin kuɗi, sayar da shaguna, da karkatar da takin zamani da aka ware wa ƙaramar hukumar, tare da wasu zarge-zarge daban.
Lawan ya bayyana cewa ko da yake shugaban ya ƙi amincewa da waɗannan zarge-zargen, ‘yan majalisar bisa ga Sashe na 128 na Kundin Tsarin Mulki da kuma Sashe na 55 (1–6) na Dokar Kananan Hukumomi ta Kano ta 2006, sun ba da shawarar a dakatar da shi na tsawon watanni uku domin gudanar da cikakken bincike.
Sauran shawarwarin sun haɗa da miƙa cikakken bayanin kuɗin shekarar 2025 na Karamar Hukumar Rano cikin gaggawa, da kuma naɗa mataimakin shugaban ya rike mukamin na wucin gadi yayin dakatarwar.
Bayan tattaunawa mai zurfi, majalisar ta amince da shawarwarin kwamitin, wanda hakan ya jawo dakatar da shugaban tare da sanya ƙaramar hukumar ƙarƙashin kulawa ta wucin gadi.
Daga Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Rano
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha
Majalisar dokokin tarayyar Turai ta amince wa kasashen nahiyar su kakkabo jiragen yakin kasar Rasha wadanda suke keta sararin samaniyar wasu daga cikin kasashen Nahiyar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa majalisar ta dauki wannan matakin ne bayan da ta sami rahotanni daga wasu daga cikin kasashen gabacin turai kan cewa jiragen yakin kasar Rasha samfurin Mig 31 da Su 25 keta sararin samaniyar kasashensu.
Firay ministan kasar Poland Donal Tusk ya ce kasarsa a shirye take ta kakkabo duk wani abu da ya shiga sararin samaniyar kasar ba tare da izini ba.
A taron majalisar don tattauna wannan batun dai wakilai 469 sun amince da bukatar a yayinda wasu 97 suka ki amincewa, sai kuma 38 wadanda suka ki kada kuri’unsu.
Jiragen yakin kasar Rasha masu tsananin sauri sun keta sararin samaniyar kasashen Poland, Estonia, Latvia, Lithuania, da kuma Romania. Sannan jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa na kasar ta Rasha sun keta sararin samaniyar kasashen Denmark, Sweden, and Norway.
Labarin yace jiragen yakin Rasha samfurin MiG-31 guda uku sun keta sararin samaniyar kasar Estonia a ranar 19 gawatan satumban da ya gabata, sannan an gawa wani jirgin Rasha yana shawagi kan kamfanin manfetur da gasa mai suna ‘ Petrobaltic oil and gas platform a kasar Poland ba tare da izini ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa October 10, 2025 Falasdinawa Daga Kudancin Gaza Sun Fara Komawa Gidajensu Da Aka Rusa A Arewacin Yankin October 10, 2025 Rahotanni : Isra’ila ta fara janye dawa wasu yankuna na Gaza October 10, 2025 Amurka ta kakaba wa wasu kamfanoni 50 takunkumi saboda sayen man Iran October 10, 2025 Isra’ila ta ce yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta fara aiki October 10, 2025 Mohajirani: Iran na goyon bayan shawarar Falastinawa kan batun dakatar da bude wuta October 10, 2025 Khalil al-Hayya: Mun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta dindindin October 10, 2025 Ministan mai na Nijar ya gana da Jakadan Iran a Yamai October 10, 2025 Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da Trump ya gabatar October 10, 2025 Guterres ya jaddada wajabcin aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci